Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci
Published: 3rd, September 2025 GMT
Kazalika, wannan biki na tunawa da nasarar fatattakar zalunci yana tunatar da mu mahimmancin waiwaye a kan tarihi. Fina-finai da aka yi game da hakan kamar “Dead to Rights”, da bikin nune-nunen a sassan yankin Macao, da faretin soja a birnin Beijing, hidindimu ne na sake duba tarihi, da sadaukarwar al’ummomin da suka gabata domin ci gaba da zaburar da na yanzu da wadanda za su zo gaba.
Birnin Beijing ya cika da annashuwa da alfahari yayin da dandalin Tian’anmen ya shaida gagarumin faretin soji domin bikin na yau. An yi gaisuwar ban-girma ta hanyar harba bindigogi 80 a sassan babban birnin domin karrama mazan jiya da suka kwanta dama da kuma wadanda suke raye. Sojoji sun yi tattaki cikin tsari mai kyau, jiragen sama sun yi fenti mai launin ja da zinariya a sararin sama, kuma tsoffin sojoji da suka halarci bikin sun kasance a matsayin shaida na jajircewa.
Shagulgulan al’adu da shirye-shiryen gidajen rediyo da talabijin da aka watsa a sassan kasar har ma da duniya baki daya sun kara raya ruhin tunawa da wannan nasara a cikin gidaje da zukatan jama’a a fadin kasar da sauran abokai na kasa da kasa. Yanayin yau a kasar Sin ya kasance na biki mai matukar armashi da ke kara girman kishin kasa tare da girmamawa ga sadaukarwar da aka yi shekaru 80 da suka gabata.
Darussan wannan tarihi a bayyane suke, wato hadin kai wajen fuskantar zalunci da kuma kiyaye mutunci domin tabbatar da adalci a doron kasa kuma tabbas, kasar Sin ta nuna gado mai kyau ta wannan fuska. Don haka, ya kamata wannan rana ta zama ba lokacin tunani ne kawai a kan nasarar da aka samu ba, amma a kan abin da ya zama wajibi a kiyaye shi. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Matashi ya rasa ransa a kan soyayya a Yobe
Wani matashi mai shekaru 20, Jibrin Saidu Lamido, ya rasa ransa bayan wani rikici a kan soyayya da ya auku ƙauyen Gurdadi da ke Ƙaramar Hukumar Yusufari a Jihar Yobe.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Talata, lokacin da Jibrin ya je zance wajen budurwarsa Saratu Gata, mai shekaru 22, a ƙauyen Kalameri.
Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35 Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — GwamnatiWata majiya ta ce wani mutum da ba a san ko waye ba ya zo wajensu, tare da tafiya da budurwar sannan ya ƙalubalanci Jibrin da ya biyo su idan shi “namijin gaske ne.”
Daga nan ne rikici ya ɓarke tsakaninsu, inda wanda ake zargi ya daɓa wa Jibrin adda a wuya.
“An garzaya da shi zuwa asibitin Kumaganam amma likita ya tabbatar da mutuwarsa,” in ji majiyar ’yan sanda.
Rundunar ’yan sandan jihar ta miƙa gawar mamacin ga iyayensa don yi masa jana’iza.
Kakakin rundunar, DSP Dungus Abdulkarim, ya tabbatar da cewa suna ci gaba da neman wanda ake zargi, wanda ya tsere bayan aikata laifin.