Aminiya:
2025-09-17@21:51:40 GMT

An kama ɗan shekara 60 kan yi wa mai shekara 24 fyaɗe

Published: 1st, September 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Legas ta kama wani dattijo mai shekaru 60, Ajayi Femi, bisa zargin yi wa wata budurwa mai shekaru 24 fyaɗe.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin a jiya Lahadi.

An kashe mutum 5 an sace limamai da hakimi a Sakkwato Simon Ekpa: An ɗaure ɗan Nijeriya kan laifin ta’addanci a Finland

Ya bayyana cewa an gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu ta hannun sashen da ke bincike cin zarafin mata na rundunar da ke Ikeja.

A cewar Hundeyin, lamarin ya faru ne a ranar 22 ga watan Agusta, 2025, inda ƙanwar wacce abin ya faru da ita ta kai rahoto ofishin ‘yan sanda na Meiran, daga nan kuma aka miƙa lamarin zuwa sashen bincike na musamman.

Binciken farko da ya haɗa da gwajin likitoci ya nuna cewa wanda ake zargi ya zuba wani abu a cikin abin sha na budurwar, wanda ya sanya ta suma, kafin ya aikata lalata da ita ba tare da amincewarta ba.

“Tuni aka gurfanar da shi gaban kotu inda aka ajiye shi a gidan yari har zuwa lokacin da aka sa ranar sake zama,” in ji Hundeyin.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Lagos, CP Olohundare Jimoh, ya bayyana cewa rundunar ta kuduri aniyar ganin an samu adalci ga duk wanda aka ci zarafinsa, tare da tabbatar da tsaron rayuka da mutuncin al’ummar jihar.

Ya kuma yi kira ga jama’a da su riƙa kai rahoton duk wani laifi da ya shafi fyaɗe ko cin zarafi zuwa mahukunta mafi kusa domin a ɗauki mataki cikin gaggawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: fyaɗe Jihar Legas

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara