Kwana 70 da ƙaddamar da taraktoci 2,000 na gwamnati har yanzu manoma ba su ga komai ba
Published: 1st, September 2025 GMT
Yanzu an fi wata biyu da Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da taraktoci 2,000 da sauran kayan aikin gona domin haɓaka harkar noma, amma manoma sun ce har yanzu ba a raba musu su ba, abin da ke iya jawo asarar daminar bana.
Ganin cewa a halin daminar tana gab da ƙarewa, manoma suna ganin lokaci ya riga ya ƙure.
Da yake ƙorafi kan lamarin, Shugaban Ƙungiyar Manoma ta Najeriya (AFAN), Injiniya Kabiru Ibrahim ya ce, “Ina rokon gwamnati ta hanzarta. Wannan shekarar ce ta gwaji wajen tabbatar da tsaron abinci.”
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewa maso Gabas (NEGF) ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ƙara tallafin kayayyakin noman damina da na rani.
NAJERIYA A YAU: Me Sakamakon Zaben Ribas Ke Nunawa Game Da Sulhun Wike Da Fubara? Rushe Kasuwar Alaba Rago: ‘A biya ’yan Arewa diyya’Taron ƙungiyar da ya gudana a Jalingo, Jihar Taraba a ƙarshen makon jiya, ya bayyana cewa tsadar kayayyakin noma da matsalar jinƙai na ƙara tsananta barazanar ƙarancin abinci.
Gwamnonin sun buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ƙara tallafin noman rani tare da tabbatar da kayan aikin sun isa ga manoma ba tare da jinkiri ba.
Yadda aka ƙaddamar da kayan aikin nomanA ranar 24 ga watan Yuni, 2025, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da shirin injinan noma a ƙarƙashin Shirin Fata Sabon Gobe, inda aka kawo taraktoci 2,000 daga ƙasar Belarus tare da kayan gyara, injinan girbi da sauransu.
Gwamnati ta ce za a yi amfani da taraktocin wajen noma hekta 550,000 da samar da ayyukan yi 16,000 da kuma taimaka wa iyalan manoma fiye da dubu 550.
Sai dai bincikenmu ya gano cewa har yanzu taraktocin suna an a ajiye a Cibiyar Hukumar Inganta Irin Noma ta Kasa (NASC) da ke Abuja.
Manoma na ƙorafi
Shugaban Kungiyar Manoma ta Najeriya (AFAN), Injiniya Kabiru Ibrahim, ya ce: “Abin mamaki ne har yanzu ba a raba taraktocin ba. Muna riƙon gwamnati ta hanzarta raba su ta hanyar da ta dace domin kada daminar bana ta wuce.”
Haka ma Dakta Ogbo Douglas, shugaban Kungiyar Manoma Maso Rajin Ci-gaban (AFPA), ya bayyana jinkirin a matsayin “abin takaici.”
Izinin Fadar Shugaban Ƙasa muke jira — MinistaWasu manyan jami’an Ma’aikatar Aikin Gona ta Tarayya sun shaida wa Wakilinmu cewa an gama tsara yadda za a raba taraktocin jiha-jiha, amma ana jiran sahalewar Fadar Shugaban Ƙasa.
Ministan Aikin Gona, Sanata Abubakar Kyari, ya ce, “Za mu tabbatar da cewa taraktocin za su yi aiki sosai ba wai a ajiye kawai ba. Da zarar mun samu izini, za mu fitar da tsarin farashin da zai zama mai sauƙi ga manoma,” in ji shi.
A baya ma an sha yi wa manoma irin wannan alƙawarin amma ba tare da an cika ba.
A 2018, an yi alƙawarin kawo taraktoci 10,000 daga kamfanin John Deere, sannan a 2021 aka ce za a kawo taraktoci 60,000, amma ba a aiwatar ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Noman rani taraktoci
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.