An kama direban mota da jabun kuɗin N1m a Oyo
Published: 30th, August 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo, ta kama wani direban mota ɗauke da jabun kuɗi har Naira miliyan ɗaya.
Kakakin rundunar, CSP Adewale Osifeso ne, ya bayyana hakan a ranar Asabar cewa jami’an sintiri na Gwamnatin Tarayya ne suka tsayar da direban a kusa da gidan Guru Maharaji, kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.
Direban mai suna Akande, ya fito daga Legas ne, kuma yana kan hanyarsa ta zuwa Osogbo, babban birnin Jihar Osun, kafin shiga hannu a ranar Juma’a.
A cewar Osifeso, lokacin da aka tsayar da motar, direban ya fara rawar jiki abin da ya sa jami’an suka binciki motarsa, inda suka gano kuɗin a cikin wata leda.
Mota da yake tafiya da ita ƙirar Toyota Sienna ce mai lambar FKJ 443 YG.
Akande, ya amsa cewa wani mutum ne ya ba shi kayan a garejin Ojota, Legas, inda aka ce man shafawa ne da za a kai Osogbo.
Amma da aka bincika, aka gano duk jabun sabbin kuɗaɗe ne masu lambobi 235923, 235922, da 235921.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda
এছাড়াও পড়ুন:
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp