Aminiya:
2025-09-18@00:34:05 GMT

An kama direban mota da jabun kuɗin N1m a Oyo

Published: 30th, August 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo, ta kama wani direban mota ɗauke da jabun kuɗi har Naira miliyan ɗaya.

Kakakin rundunar, CSP Adewale Osifeso ne, ya bayyana hakan a ranar Asabar cewa jami’an sintiri na Gwamnatin Tarayya ne suka tsayar da direban a kusa da gidan Guru Maharaji, kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.

Mutum 13 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Zamfara  Jigon jam’iyyar PDP a Gombe, Haruna Jonga, ya koma APC

Direban mai suna Akande, ya fito daga Legas ne, kuma yana kan hanyarsa ta zuwa Osogbo, babban birnin Jihar Osun, kafin shiga hannu a ranar Juma’a.

A cewar Osifeso, lokacin da aka tsayar da motar, direban ya fara rawar jiki abin da ya sa jami’an suka binciki motarsa, inda suka gano kuɗin a cikin wata leda.

Mota da yake tafiya da ita ƙirar Toyota Sienna ce mai lambar FKJ 443 YG.

Akande, ya amsa cewa wani mutum ne ya ba shi kayan a garejin Ojota, Legas, inda aka ce man shafawa ne da za a kai Osogbo.

Amma da aka bincika, aka gano duk jabun sabbin kuɗaɗe ne masu lambobi 235923, 235922, da 235921.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin