Mutum 13 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Zamfara
Published: 30th, August 2025 GMT
Aƙalla mutum 13 ne suka rasu, yayin da sama da 20 suka ɓace a Jihar Zamfara, bayan jirgin ruwan da suka hau domin tsere wa ’yan bindiga ya nutse.
Mazauna yankin da wasu jami’ai sun tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Asabar.
Jigon jam’iyyar PDP a Gombe, Haruna Jonga, ya koma APC Dokar ta-ɓaci: Fubara zai dawo ofis ranar 18 ga Satumba — WikeHarin ya faru ne a ranar Juma’a a yankin Birnin Magaji, inda ’yan bindiga suka kai wa ƙauyuka biyu hari.
Mutane da dama ne suka tsere zuwa bakin kogi, inda suka riski jirgin ruwa guda ɗaya kacal.
Hakan ya sa aka jirgin da mutane sosai, lamarin da ya sa ya nutse a cikin ruwa.
“Babban yayana da ’ya’yan yayata biyu suna cikin waɗanda suka rasu,” in ji Shehu Mohammed, wani ma’aikacin lafiya a Birnin Magaji.
Sarkin yankin, Maidamma Dankilo, ya tabbatar da rasuwar mutum 13.
Amma ya ce an ceto mutum 22, sauran 22 kuma har yanzu ba a gan su ba.
Zamfara ta daɗe tana fama da hare-haren ’yan bindiga.
A makon da ya gabata, ’yan bindiga sun kashe mutum biyu tare da sace sama da 100 a wani hari da suka kai kimanin kilomita 150 daga Birnin Magaji.
Rahotanni sun nuna cewar Jihar Zamfara ta fuskanci hare-haren ’yan bindiga sama da 50 tsakanin Yulin 2024 zuwa Yunin 2025, inda aka sace mutane sama da 1,000.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari Jirgin ruwa Zamfara yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da fasinjoji a cikin wasu motocin bas Toyota guda biyu a titin Itobe zuwa Ajegwu-Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu ta jihar Kogi.
An samu rahoton cewa, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 5 na asubahi a tsakanin ƙauyukan Ojiwo’-Ajengo da Mamereboh da ke kan babbar hanyar.
Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasaAn ce masu garkuwa da mutanen sun yi amfani da wata tirela da aka kama wajen tare hanyar bayan shingen binciken jami’an tsaro, da ke kusa da wurin da lamarin ya faru.
Shedun gani da ido sun ce ɗaya daga cikin motocin bas ɗin mai lamba KG: KPA 622LG na kan hanyarta zuwa Abuja, tare da fasinjoji daga wata tashar mota a unguwar Ankpa da ke yankin Kogi ta Gabas.
Har yanzu ba a iya gano adadin fasinjojin da aka yi garkuwa da su ba zuwa yanzu, sai dai mun iya tabbatar da cewa ɗaya daga cikin motocin na ɗauke da fasinjoji ne daga yankin Ankpa, kamar yadda aka gano wasu takardu da wasu kayayyaki a wurin da lamarin ya faru suka bayyana.
“Motocin bas ɗin guda biyu suna kan hanyar Abuja ne a lokacin da suka ci karo da shingayen ’yan bindiga a safiyar ranar Alhamis. Dukkanin fasinjojin, ciki har da direban motocin bas ɗin biyu an yi awon gaba da su cikin daji,” in ji Unubi Ademu, wani mazaunin Achigili, a ƙauyen da ke maƙwabta.
Al’ummar yankin sun ƙara da cewa, jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da mafarauta da kuma ’yan banga suna ƙoƙarin magance lamarin.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Kogi (PPRO), CSP William Aya bai amsa kira da saƙo ba lokacin da aka tuntuɓe shi har zuwa lokacin tattatara wannan rahoto.