Aminiya:
2025-09-17@21:51:34 GMT

Mutum 13 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Zamfara 

Published: 30th, August 2025 GMT

Aƙalla mutum 13 ne suka rasu, yayin da sama da 20 suka ɓace a Jihar Zamfara, bayan jirgin ruwan da suka hau domin tsere wa ’yan bindiga ya nutse.

Mazauna yankin da wasu jami’ai sun tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Asabar.

Jigon jam’iyyar PDP a Gombe, Haruna Jonga, ya koma APC Dokar ta-ɓaci: Fubara zai dawo ofis ranar 18 ga Satumba — Wike

Harin ya faru ne a ranar Juma’a a yankin Birnin Magaji, inda ’yan bindiga suka kai wa ƙauyuka biyu hari.

Mutane da dama ne suka tsere zuwa bakin kogi, inda suka riski jirgin ruwa guda ɗaya kacal.

Hakan ya sa aka jirgin da mutane sosai, lamarin da ya sa ya nutse a cikin ruwa.

“Babban yayana da ’ya’yan yayata biyu suna cikin waɗanda suka rasu,” in ji Shehu Mohammed, wani ma’aikacin lafiya a Birnin Magaji.

Sarkin yankin, Maidamma Dankilo, ya tabbatar da rasuwar mutum 13.

Amma ya ce an ceto mutum 22, sauran 22 kuma har yanzu ba a gan su ba.

Zamfara ta daɗe tana fama da hare-haren ’yan bindiga.

A makon da ya gabata, ’yan bindiga sun kashe mutum biyu tare da sace sama da 100 a wani hari da suka kai kimanin kilomita 150 daga Birnin Magaji.

Rahotanni sun nuna cewar Jihar Zamfara ta fuskanci hare-haren ’yan bindiga sama da 50 tsakanin Yulin 2024 zuwa Yunin 2025, inda aka sace mutane sama da 1,000.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari Jirgin ruwa Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

 

A yayin samamen, kakakin ‘yansandan Neja ya ce an kama mutane shida a wurin da ake hakar ma’adinan yayin da wasu kuma suka tsere.

 

Abiodun ya bayyana sunayen wadanda ake cafken da Aliyu Rabiu, Samaila Ibrahim, Sadiku Auwal, Ibrahim Babangida, Musa Adamu da Sani Hassan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara