“Al’ummar kasa da kasa da yawa sun sauya ra’ayinsu mai kyau game da Amurka zuwa mummunan ra’ayi, yayin da yawan masu nuna kauna ga kasar Sin ya karu.” Wani bincike da kamfanin bincike na Morning Consult na Amurka ya fitar kwanan nan ya nuna cewa, har zuwa karshen watan Mayu, yawan al’ummar duniya dake nuna kauna ga Amurka ya ragu zuwa -1.

5, yayin da adadin ya karu zuwa 8.8 ga kasar Sin. Ko da yake sakamakon ya fito ne daga hukumar bincike guda daya kawai, amma yana da ma’ana sosai wajen yin kashedi, idan aka yi la’akari da cewa binciken ya shafi kasashe da yankuna fiye da arba’in, inda akasarinsu su ne muhimman abokan huldar Amurka a fannin tattalin arziki da aikin soja.

Wannan sakamakon ba wani abu ne da ya faru ba zato ba tsammani ba. Tun daga farkon bana, matakin kakaba haraji da Amurka ta dauka ba bisa ka’ida ba ya kawo jerin munanan tasirori, wanda ya haifar da illa ga tattalin arzikin duniya, kuma Amurka ita kanta ta sha wahala daga irin wannan matakin.

Su wane ne masu lalata cinikin duniya? Su wane ne masu kare ciniki cikin ’yanci? Jama’ar duniya sun sani a bayyane.

Yanzu dai kasashe da yawa sun gane cewa, manufar “Amurka gaba da kome” ba za ta haifar da kome ba sai rikice-rikice kawai, kuma mika wuya ga matakin zaluncin haraji‌ zai haifar da karin matsawa‌ kawai. Sai dai ta hanyar hadin kai, dogaro da kai da nemo cimma nasara tare ne kawai za su iya kare hakkokinsu da muradunsu da ma samun ci gaba tare. Wannan binciken jin ra’ayin jama’a gargadi ne da duniya ya yi ga Amurka, wato idan ta ci gaba da shagala da ra’ayin samun riba kan asarar wani bangare, za ta rasa dukkan kasashe masu kawance da ita. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO

Su kuwa mahalarta taron, sun yaba da kyautatuwar dangantakar kasashen biyu da rawar da SCO ke takawa. Sun kuma bayyana fatan Masar da Sin za su yi amfani da damarmakin ci gaba da SCO ta samar domin su hada hannu tare, su inganta tsarin jagorantar harkokin duniya da farfadowar kasashe masu tasowa. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da  Falasdinu a matsayin Mamba
  • Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
  • Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO
  • PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne