Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji
Published: 4th, June 2025 GMT
An gano gawar yara bakwai a yankin Mokwa, da ke Jihar Neja, bayan ambaliyar ruwa da ta afka wa garin mako guda da ya wuce.
Yawan adadin waɗanda suka rasu kawo yanzu ya kai mutum 160, amma wasu jami’ai sun ce za a iya gano gawar sama da mutum 200.
Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan SandaAmbaliyar ta kuma tafi da motar haya mai kujeru 18 ɗauke da fasinjoji.
Kawo yanzu, bayan kwana shida da faruwar ambaliyar, ba a ga motar ko wani daga cikin fasinjojin ba.
Wani mazaunin garin, Baba Abu, ya ce: “Direban bai nemi ƙetare ruwan ba. Ya tsaya gefe yana jira ruwa ya ragu.
“Amma sai ruwan ya ƙaru ya kwashe motar ya jefa ta cikin Kogin Neja. Har yanzu ba mu san inda ta ke ba.”
Wasu daga cikin waɗanda ambaliyar ta shafa sun koka cewa ba sa samun kayan tallafi, duk da cewa gwamnati ta ce tana rabawa.
Hadiza Saidu, wadda ta rasa mahaifiyarta da komai nata, ta ce: “Da kayan jikina guda ɗaha da hijabi na tsira da su. Idan muka je karɓar tallafi, sai a ce ya ƙare. Wasu da ambaliyar ba ta shafa ba ake bai wa tallafin.”
Mutane sun fusata bayan wasu manyan cirarun jami’an gwamnati ne kawai suka ziyarci Minna, ba tare da sun je Mokwa inda ambaliyar ta faru ba.
Ƙungiyoyi da mazauna yankin sun ce hakan bai nuna an tausaya waɗanda lamarin ya shafa ba.
Gwamnati ta ce ambaliyar ta samo asali ne daga ruwan sama mai ƙarfi da kuma lalatacciyar hanyar ruwa, ba daga buɗe dam ba.
Masana da Ƙungiyar Tsofaffin Arewa (NEF), sun buƙaci gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa don taimaka wa waɗanda lamarin ya shafa da kuma kare sake faruwar hakan a gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa gwamnati Mokwa da ambaliyar ambaliyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bayyana cewa: Babu wata tattaunawa da zata yi da Amurka a halin da take ciki na kare kanta
A yayin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan yankunan kasar Iran, a hukumance Iran ta bayyana rashin yiwuwar ci gaba da zaman tattaunawa da Amurka kan batun shirinta na makamshin nukuliya, tare da dora wa Amurka alhakin abin da ke faruwa kai tsaye.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Akwai hadin kai tsakanin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka wajen kai hare-hare kan kasar Iran domin rusa zaman tattaunawar nukiliya da haka ke bayyana kawar da duk wata magana ta hakikanin aniyar Amurka na samar da hanyar warware takaddamar Shirin Iran ta hanyar lumana.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa ci gaba da tattaunawa da Amurka a yayin da ake ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri yana gwada tsarin tattaunawar ba shi da ma’ana. Ya yi kakkausar suka ga matakin da hukumar ta IAEA ta dauka, inda ya yi la’akari da hakan a matsayin wani dalili na halasta cin zarafi a kan cibiyoyin nukiliyar Iran.