Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji
Published: 4th, June 2025 GMT
An gano gawar yara bakwai a yankin Mokwa, da ke Jihar Neja, bayan ambaliyar ruwa da ta afka wa garin mako guda da ya wuce.
Yawan adadin waɗanda suka rasu kawo yanzu ya kai mutum 160, amma wasu jami’ai sun ce za a iya gano gawar sama da mutum 200.
Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan SandaAmbaliyar ta kuma tafi da motar haya mai kujeru 18 ɗauke da fasinjoji.
Kawo yanzu, bayan kwana shida da faruwar ambaliyar, ba a ga motar ko wani daga cikin fasinjojin ba.
Wani mazaunin garin, Baba Abu, ya ce: “Direban bai nemi ƙetare ruwan ba. Ya tsaya gefe yana jira ruwa ya ragu.
“Amma sai ruwan ya ƙaru ya kwashe motar ya jefa ta cikin Kogin Neja. Har yanzu ba mu san inda ta ke ba.”
Wasu daga cikin waɗanda ambaliyar ta shafa sun koka cewa ba sa samun kayan tallafi, duk da cewa gwamnati ta ce tana rabawa.
Hadiza Saidu, wadda ta rasa mahaifiyarta da komai nata, ta ce: “Da kayan jikina guda ɗaha da hijabi na tsira da su. Idan muka je karɓar tallafi, sai a ce ya ƙare. Wasu da ambaliyar ba ta shafa ba ake bai wa tallafin.”
Mutane sun fusata bayan wasu manyan cirarun jami’an gwamnati ne kawai suka ziyarci Minna, ba tare da sun je Mokwa inda ambaliyar ta faru ba.
Ƙungiyoyi da mazauna yankin sun ce hakan bai nuna an tausaya waɗanda lamarin ya shafa ba.
Gwamnati ta ce ambaliyar ta samo asali ne daga ruwan sama mai ƙarfi da kuma lalatacciyar hanyar ruwa, ba daga buɗe dam ba.
Masana da Ƙungiyar Tsofaffin Arewa (NEF), sun buƙaci gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa don taimaka wa waɗanda lamarin ya shafa da kuma kare sake faruwar hakan a gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa gwamnati Mokwa da ambaliyar ambaliyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22
Ya ƙara da cewa FRSC ta fara bincike kan dalilan da ke jawo hatsarin, kuma za ta gabatar da sakamakon binciken ga hedikwatarta da kuma Gwamnatin Jihar Kano domin ɗaukar matakan da suka dace don hana irin faruwar irin wannan iftila’i a gaba.
Hukumar ta kuma sake jaddada ƙudirinta na wayar da kan al’umma kan amfani da hanya yadda ya dace da kiyaye lafiyar masu amfani da hanya.
A nasa ɓangaren, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Gwarzo, ya wakilta, ya gode wa FRSC bisa ziyarar.
Ya bayyana damuwarsa cewa wajen da hatsarin ya faru ya daɗe yana haddasa mummunan haɗura, inda ya bayyana cewa gwamnati za ta yi duk abin da ya kamata don hana faruwar hakan a nan gaba.
“Idan kun san wani waje da ke da hatsari a cikin gari ko wajen gari, ka da ku yi shiru. Ku sanar da gwamnati. Wannan aiki ne da za mu tashi gaba ɗaya domin shawo kansa,” in ji shi.
Ya bayyana mutuwar ‘yan wasan 22 a matsayin abin firgici da tashin hankali, yana mai cewa ziyarar da FRSC ta kai ya nuna alhini da tausayi ga al’ummar Kano da iyalan waɗanda lamarin ya shafa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp