Leadership News Hausa:
2025-06-22@16:54:28 GMT

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Published: 5th, June 2025 GMT

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Da safiyar yau Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da takwaransa na kasar Belarus Aleksandr Lukashenko a nan birnin Beijing. Yayin ganawar tasu, Xi Jinping ya sake taya takwaran nasa na Belarus Aleksandr Lukashenko murnar nasarar yin tazarce.

Xi ya ce, Sin na daukar huldar sassan biyu da muhimmanci, kuma tana raya ta bisa hangen nesa kan manyan tsare-tsare, tare da fatan kara hadin gwiwa da Belarus, don gaggauta bunkasa huldarsu, da ma cimma moriya tare cikin hadin gwiwa.

Ya kara da cewa, dole ne kasashen biyu su kara hadin kai, da marawa juna baya karkashin kungiyoyin kasa da kasa, ciki har da MDD da SCO da sauransu, don taka rawarsu tare wajen dakile babakere, da kiyaye adalci da daidaito a dukkanin fadin duniya.

A nasa bangare kuwa, mista Lukashenko ya ce, wannan ne karo na 15 da yake gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin, kuma a ko wane karo yana kara fahimtar dankon zumunci dake tsakaninsu. Ya ce Belarus na matukar godiya bisa daddaden taimakon da Sin ke bayarwa gare ta, yana mai fatan raya huldar kasashen biyu ba tare da tangarda ba, da ma gaggauta hadin gwiwarsu a mabambantan bangarori. (Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’

Fadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai zabi wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2027 a hukumance ne kawai bayan a kammala babban taron jam’iyyar APC a 2026.

Kakakin shugaban, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawarsa da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.

Da yake martani kan dalilin da ya sa fadar shugaban ta yi shiru kan zargin cewa Tinubu na son canza mataimaki a 2027 musamman la’akari da yadda ’yan jam’iyyar ke ta nuna goyon bayansu ga shugaban shi kadai, Onanuga ya ce hakan ba gaskiya ba ne.

Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya

A cewarsa, “Lokacin da na karanta labarin, na karyata shi saboda ba shi da tushe. A tsarin shugaba mai cikakken iko da Najeriya ke bi, dan takarar shugaban kasa ake fara zaba, shi kuma sai ya zabi wanda zai yi masa mataimaki. Abin da ya faru ke nan a lokacin Buhari – an fara zabensa, sai daga baya shi kuma ya dauki mataimaki. Ba a yin duka biyun a lokaci daya.

“Da zarar INEC ta fitar da jadawalin zabuka, jam’iyya za ta shirya babban taronta, idan aka sake tsayar da shugaban kasa, shi kuma zai zabi mataimakinsa,” in ji Onanuga.

Kazalika, ya kuma yi fatali da tarihin da ake daukowa cewa sau biyu tinubu yana canza mataimaka lokacin da ya yi Gwamna a jihar Legas daga 1999 zuwa 2007, cewa irin haka za ta faru da Kashim Shettima a 2027.

Ya kuma ce jita-jitar da ake yadawa a kan yiwuwar canza Shettima tun ma kafin a fara nuna amincewa da sake takarar Tinubu ba ta da tushe.

Ya ce, “Ba ni da masaniya a kan duk wani sabani tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa. Iya abin da na sani shi ne akwai kyakkyawar fahimtar juna da alakar aiki mai kyau a tsakaninsu. Duk maganganun da ake yadawa ba su da maraba da na teburin mai shayi. Mutane na ta fadara maganganun rashin kan gado cewa wai Seyi Tinubu ne ma mataimakin shugaban kasa. Wannan shashanci ne.

“A wannan kasar, mukamin mataimaka ko na gwamna ko na shugaban kasa ba a raba su da ’yan tsegungumin mutane. Ko da ana zaune lafiya babu wata matsala, makunsantansu sai sun kirkiri husuma da labaran karya. Amma iya abin da na sani shi ne babu matsala tsakanin Tinubu da Shettima.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran
  • Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
  • Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump