Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Published: 5th, June 2025 GMT
Da safiyar yau Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da takwaransa na kasar Belarus Aleksandr Lukashenko a nan birnin Beijing. Yayin ganawar tasu, Xi Jinping ya sake taya takwaran nasa na Belarus Aleksandr Lukashenko murnar nasarar yin tazarce.
Xi ya ce, Sin na daukar huldar sassan biyu da muhimmanci, kuma tana raya ta bisa hangen nesa kan manyan tsare-tsare, tare da fatan kara hadin gwiwa da Belarus, don gaggauta bunkasa huldarsu, da ma cimma moriya tare cikin hadin gwiwa.
A nasa bangare kuwa, mista Lukashenko ya ce, wannan ne karo na 15 da yake gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin, kuma a ko wane karo yana kara fahimtar dankon zumunci dake tsakaninsu. Ya ce Belarus na matukar godiya bisa daddaden taimakon da Sin ke bayarwa gare ta, yana mai fatan raya huldar kasashen biyu ba tare da tangarda ba, da ma gaggauta hadin gwiwarsu a mabambantan bangarori. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
Ana zargin wata uwa a jihar Enugu da kashe ’ya’yanta biyu saboda tsananin kuncin rayuwa.
Lamarin ya faru a unguwar Trans Ekulu da ke yankin birnin na Enugu.
An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisaAn ga gawarwakin yara biyu a gidan lokacin da jami’an tsaro sukashiga ciki, lamarin da ya tayar da hankulan jama’ar unguwar.
Yaran da ake zargin uwar tasu da kashewa sun hada da yarinya mai suna Esther Arinze mai shekara hudu da haihuwa da kuma kaninta mai suna Chibusoma.
Ana zargin an yi amfani da makami mai kaifin gaske wajen ji wa yaran raunuka a jikunansu kafin su rasu.
Majiyar labarinmu da rundunar ’yan sandan yankin Trans Ekulu sun amsa kiran gaggawar ne daga unguwar aka shaida musu faruwar lamarin inda su kuma ba su yi kasa a gwiwa ba suka rankaya zuwa gidan inda suka iske gawarwakin yara jina-jina.
Daga bisani dai ’yan sanda sun kwashe gawarwakin yaran zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Enugu, inda likitoci suka tabbatar da mutuwar su.