Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Nain Qasim da kuma ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi sun gana a birnin Beirut babban birnin kasar Lebanon inda bangarorin biyu suka tattauna al-amuran siyasa da yankin kudancin Asiya tare da kasar Lebanon.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto aragchi yana cewa dangantaka tsakanin Iran da kungiyar Hizbullah dangane ce wacce ta shafi yankin kudancin Asiya gaba daya.

A nashi bangaren shugaban kungiyar Hizbullah sheikh Naem Kassem ya godewa JMI ta irin tallafin da take bayarwa ga kungiyoyi da kasashen kawancen masu gwagwarmaya a yankin wadanda suka hada da Falasdinawa da Lebanon da sauransu.

Aragchi ya kara da cewa Iran a shirye take ta taimakawa kasar Lebanon a harkokin siyasa tattalin arziki da zamantakewa. Ya kuma yabawa kungiyar Hizbullah kan rawan da take takawa wajen tabbatar da tsaro da kuam zaman lafiya a kasar Lebanon, musamman da HKI wacce take mamaye da wasu yankunan na kasar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kungiyar Hizbullah a kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Hare Kan Yankunan Siriya Musamman Yankin Kudancin Kasar

Sojojin mamayar Isra’ila sun sanar da kaddamar da farmaki kan yankin  kudancin Siriya

Sojojin mamayar Isra’ila sun sanar da cewa: Da sanyin safiyar yau Laraba, jiragen yakinsu suka kaddamar da farmaki kan wasu wuraren soji a kudancin Siriya, kuma sun dora alhakin halin da ake ciki a kan gwamnatin Ahmed al-Sharaa.

Rundunar sojin mamayar Isra’ila a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce: A wani lokaci kadan da ya gabata, bayan kai hare-hare kan yankunan haramtacciyar kasar Isra’ila, jiragen saman yakin na haramtacciyar kasar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a wuraren makaman gwamnatin Siriya a kudancin kasar ta Siriya.

Ta kara da cewa: Halaltacciyar gwamnati ce ke da alhakin halin da ake ciki a kasar Siriya, kuma za ta ci gaba da daukar nauyinta muddin aka ci gaba da nuna kyama ga yahudawan sahayoniyya daga yankinta, sojojin za su kalubalanci duk wata barazana da ke da hadari ga haramtacciyar kasar Isra’ila.

Tashar yada labarai ta kasar Siriya ta tabbatar da cewa: Jiragen saman Isra’ila sun kaddamar da farmaki a Tal Shaar da ke yankin Quneitra da ke kusa da birnin Izra da ke tsakiyar yankin Dar’a da kuma yankunan Sa’sa’ da Kanaker da ke yankin birnin Damascus fadar mulkin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Ali Shamkhani: Iran Ba Zata Taba Saryar Da Hakkinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Hare Kan Yankunan Siriya Musamman Yankin Kudancin Kasar
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar
  • Aragchi: Iran Tana Goyon Bayan Tattaunawa Saboda Hadin Kai Tsakanin Mutanen Lebanon
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Alakar Iran Da Lebanon Tarihi Ce Mai Tushe Da Ta Ginu Kan Mutunta Juna
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Soki Rahoton Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Kan Kasarsa
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
  • Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa