Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Nain Qasim da kuma ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi sun gana a birnin Beirut babban birnin kasar Lebanon inda bangarorin biyu suka tattauna al-amuran siyasa da yankin kudancin Asiya tare da kasar Lebanon.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto aragchi yana cewa dangantaka tsakanin Iran da kungiyar Hizbullah dangane ce wacce ta shafi yankin kudancin Asiya gaba daya.

A nashi bangaren shugaban kungiyar Hizbullah sheikh Naem Kassem ya godewa JMI ta irin tallafin da take bayarwa ga kungiyoyi da kasashen kawancen masu gwagwarmaya a yankin wadanda suka hada da Falasdinawa da Lebanon da sauransu.

Aragchi ya kara da cewa Iran a shirye take ta taimakawa kasar Lebanon a harkokin siyasa tattalin arziki da zamantakewa. Ya kuma yabawa kungiyar Hizbullah kan rawan da take takawa wajen tabbatar da tsaro da kuam zaman lafiya a kasar Lebanon, musamman da HKI wacce take mamaye da wasu yankunan na kasar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kungiyar Hizbullah a kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

 Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza

Kungiyar ta malaman musulumi ta fitar da fatawa da a ciki ta bukaci gwamnatoci da al’ummar musulmi da su yunkura cikin gaggawa domin kawo karshen killace yankin Gaza da aka yi, da kuma wajabcin kai musu abinci da magunguna.

Kungiyar malaman musulmin ta kuma bayyana abinda HKI take yi na killace mutanen Gaza fiye da miliyan biyu da haka su abinci da magani,musamman mata, yara da manya,wani babban laifi ne da ba shi da tamka a cikin tarihi, tana mai yin kira ga al’ummu da gwamnatoci da su motsa saboda su taimaki raunana.

Kwamitin fatawa da yake a karkashin wannan kungiyar ta malaman musulmi, ya dogara da ayoyin alkrur’ani da hadisan ma’aiki ( s.a.w) da manufofi na shari’a da ka’idoji na fikihu da su ka wajabta taimakawa wadanda aka zalunta da kawar da zaluncin da ake yi masa.

Fatawar ta kuma bayyana cewa, kin taimakawa wajen taimakawa alhali da akwai dama, yana daidai da yin tarayyar a cikin laifukan yaki.

A wani gefen, bayanin da ya fito daga kungiyar malaman musulmin ya kuma yi kira ga al’ummu da su fito domin yin zanga-zanga da zaman dirshan a gaban ofisoshin jakadancin kasashen Amurka da turai.

Har ila yau fatawar ta bukaci kasar Masar da ta dauki nauyin da ya rataya a wuyanta na tarihi da addini, ta bude mashigar Rafaha, saboda a shigar da kayan abinci da dukkanin bukatun yau da kullum. Har ila yau ta ce, yin shiru akan wannan batun shi ne;yin shiru akan wannan bala’in bai dace da ma’abota ilimi da addini.”

Wani bangare na sakon kungiyar ta malaman musulunci ya shafi yin kira ga ma’abota tunani da alkalami da su rika aikewa da sakwanni ta shafukansu domin yin matsyin lamba saboda a kawo karsehn wannan bala’in da yake faruwa a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco