Wata kotun kasar Mali ta kori karar da aka shigar a gabata, don neman soke matakin da majalisar soj0jin kasar ta dauka na rusa jam’iyyun siyasa gaba daya.

A ranar 13 ga watan Mayu ne da ya gabata ne majalsiar koli ta sojojin kasar Mali ta fitar da dokar haramta dukkan jam’iyyun siyasa a kasar wadanda yawansu ya kai 300, tare da manusar sake fasalinsu.

Wasu lauyoyi da kuma ‘yan siyasar kasar ne dai su ka shigar da karar a gaban kotu, daga cikinsu har da ‘Montagal Tal’ wanda ya kasance jagoran daya daga cikin jam’iyyun da aka majalisar sojojin ta soke.

Masu shigar da karar, sun bayyana matakin da majalisar sojan kasar ta dauka da cewa keta hurumin ‘yancin siyasa ne da kuma yencin yin taruka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed

Datti Baba-Ahmed, wanda ya yi wa Peter Obi, takarar mataimaki a zaɓen 2023, ya ce yana goyon bayan Obi idan yana so ya sake yin takara a 2027, ko da ba tare da shi ba.

Peter Obi da Datti sun tsaya takara tare a 2023 sai dai sun ƙare a na uku.

NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido

Shugaba Bola Tinubu ne ya lashe zaɓen.

Datti, ya ce Obi yana da ’yancin sake tsayawa takara a ƙarƙashin LP.

Ya kuma ce ba dole ne sai Obi ya yi haɗin gwiwa da shi ba.

“Peter Obi mutum ne da nake girmamawa ƙwarai. Yana da damar sake fitowa takara a 2027, ko da ba tare da ni ba,” in ji Datti a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels.

Datti, wa ds tsohon Sanata ne, ya ce Najeriya na buƙatar shugabanni masu gaskiya da za su iya kawo ci gaba, ba masu alƙawuran ƙarya ba.

“Muna cikin wani yanayi mai muhimmanci. ’Yan Najeriya na buƙatar aiki ba uzuri ba. Muna buƙatar shugabanni masu cika alƙawari da gyara ƙasa,” in ji shi.

Game da shigar Peter Obi a wata haɗakar siyasa a jam’iyyar ADC, Datti ya ce hakan ba laifi ba ne.

“Haɗin gwiwa a siyasa ba cin amanar jam’iyya ba ne. Hakan al’ada ce a siyasa, inda mutane da jam’iyyu ke haɗuwa don cimma buri ɗaya.

“Ni ma na halarci wasu daga cikin tarukan. Ba wani abu ba ne da ya saɓa wa doka ko tsarin jam’iyya,” in ji shi.

Ya ce wannan haɗin gwiwar na da nufin samar wa ’yan Najeriya zaɓi mai kyau duba da halin da ake ciki.

Game da batun karɓa-karɓar mulki tsakanin Arewa da Kudu, Datti, ya ce kamata ya yi shugabancin ƙasa ya koma Kudu a 2027.

Ya ce wannan ba lissafin siyasa ba ne, amma manufar adalci da haɗin kai a ƙasa mai yawan ƙabilu kamar Najeriya ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • 2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin