An lakaɗa wa Mataimakin Firinsifal duka saboda hana satar a jarabawa
Published: 2nd, June 2025 GMT
Wasu ’yan daba sun yi wa Mataimakin Firinsifal na wata makarantar sakandare dukan tsiya a wani mummunan harin da suka kai masa saboda ya hana wani ɗalibi satar jarabawa.
A yayin da ake ci gaba da jarabawar kammala sakandare ta WASSCE da ake yi a halin yanzu ne, Mista Rotifa, mataimakin shugaban wata makaranta mai zaman kanta mai suna Child Development College da ke Akure, hedikwatar Jihar Ondo, ya hana ɗalibin satar amsa.
Bayan haka ne ’yan daban sun tsare Mista Rotifa suka yi masa dukan kawo wuƙa bayan sun jawo shi daga motar ’yan sanda, kafin a ceto shi a kai shi asibiti.
Lamarin ya faru ne bayan Mista Rotifa ya ƙwace wayar salula da wani ɗalibi ke amfani da ita wajen yin satar jarabawa makon jiya.
Majiyoyi sun yi zargin cewa iyayen ɗalibin ne suka ɗauko hayar ’yan daban, bayan wata barazana da mahaifiyar ɗalibin ta yi a baya cewa za ta kai hari ga duk wanda ya hana ɗanta yin satar jarabawa.
Duk da barazanar ta farko, an ruwaito cewa makarantar ba ta ɗauki wani mataki ba har sai da aka kawo wa Mataimakin Firinsifal ɗin farmaki.
’Yan daban sun tsare Mista Rotifa sa’annan suka yi masa dukan tsiya bayan ya kai rahoton barazanar ga ’yan sanda. Sun jawo shi daga motar ’yan sanda kuma suka dake shi kafin a ceto shi a kai shi asibiti.
Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Ondo ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa an fara bincike.
Ko da yake an sallame shi daga asibiti, Mista Rotifa bai koma gida ba saboda tsaron lafiyarsa.
Hukumomi suna ƙoƙarin kama masu hannu a laifin kuma ana shirye-shiryen tabbatar da tsaron ma’aikatan makarantar da ɗalibai har zuwa ƙarshen jarabawar WASSCE.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan daba Ɗalibi Sa satar jarabawa WASSCE
এছাড়াও পড়ুন:
Magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga
’Yan bindiga sun sako wani magidanci da suka yi garkuwa da shi da amaryarsa na tsawon wata bakwai, bayan sun bindige matar tasa tare da karɓar kuɗin fansa Naira miliyan 30 daga iyalansa.
A watan Oktobar 2024 ne ’yan bindiga suka yi garkuwa da mutumin suna Yakubu Dada tare da amaryarsa, a yayin da ma’auratan ke tafiya a kan babban titin zuwa Kontagora a Jihar Neja.
A lokacin ’yan bindigar sun buƙaci kuɗin fansa Naira miliyan 10 daga iyalan mutumin, wanda tsohon ma’aikacin gwamnati ne.
Ba su sako shi ba sai a ranar Litinin, bayan da suka karɓi ƙarin Naira miliyan 20 daga iyalansa, jimilla Naira miliyan 30 ke nan.
A lokacin da suka yi garkuwa da ma’auratan sun buƙaci Naira miliyan 10, amma bayan iyalansa sun yi karo-karo sun biya, sai ’yan ta’addan suka nemi ƙarin Naira miliyan 20 da sababbin babura ƙirar Bajaj, sa’nnna suka yi barazanar kashe ma’auratan idan ba a ba su ba.
A farkon watan Mayu 2025, suka bindige amaryar tasa mai suna Lami, a ƙoƙarinsu na matsa wa iyalan su biya musu buƙata.
Uwar gidarsa mai suna Maimuna, ta tabbatar wa Aminiya cewa an sake shi a wani daji da ke kusa da yankin Kotonkoro a Ƙaramar Hukumar Mariga ta Jihar Neja, bayan da iyalan suka biya ƙarin Naira miliyan 20.
Malama Maimuna ta bayyana farin cikinsu, amma ta ce Malam Yakubu bai riga ya ya iso gida ba a lokacin.
Ta bayyana cewa a watan Nuwambar 2024 sai da suka sayar da kusan duk abin da suka mallaka domin haɗa Naira miliyan 10 da aka buƙata, wanda ƙanin mijin nasu ya kai wa ’yan bindigar a wani daji a Jihar Kebbi.
Ta ce bayan nan ne ’yan ta’ddan suka nemi ƙarin Naira miliyan 60 amma daga ƙarshe aka daidaita da su a kan Naira miliyan 20 da sababbin babura guda huɗu, buƙatar a iyalan suka yi ƙoƙarin biya kafin a sako shi.