Najeriya: An Bude Bincike Sojojin Da Suke Bayar Da Makamai Ga Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai
Published: 1st, June 2025 GMT
Mahukunta a tarayyar Najeriya sun sanar da kama wasu sojoji da ‘yan sanda 30 bisa tuhumarsu da sace makaman gwamnati da sayar da su ga kungiyoyi masu dauke da makamai, daga cikinsu har da kungiyoyin da suke ikirarin jihadi.
Sanarwar da rudnunar sojan kasar ta Najeriya ta fitar ta kunshi cewa; Farmakin da rundunar sojan kasar ta fara kai wa a cikin watan Ogusta na 2024 tana a matsayin mayar da martani ne akan satar makamai da alabarusai na gwamanti da ake yi, kuma ya zuwa yanzu bincike ya sa an kama sojoji 18 da kuma ‘yan sandan 15 sai kuma wasu fararen hula 8 da su ka hada da sarkin gargajiya daya.
Wannan sanarwar dai ta zo ne adaidai lokacin da kasar ta Najeriya take fuskantar kalubale mai girma ta fuskar tsaro, ta yadda a bayan nan kungiyoyin Bokoharam, da Iswap su ka dawo da hare-haren da suke kai wa musamman akan rundunar sojojin kasar.
Dama a baya wata cibiyar mai nazari da bincike akan yankunan da ake rikice-rikicen makamai a duniya mai matsuguni a Birtaniya, ta bayyana cewa; Kungiyoyin da suke ikirarin jihadi a yankin Sahel, suna samun kaso 20% na makamansu ne daga cikin kasashensu.
Baya ga matsalar masu ikirarin jihadi da ake fama da su da Najeriya, da akwai kuma ta barayin daji da suke sace mutane domin karbar kudin fansa, mafi yawancinsu a yankin Arewa maso yammacin kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Masu Zanga Zanga A Libya Sun Bukaci Firai Ministan Kasar Ya Sauka
Masu zanga zanga kimani makunni uku da suka gabata a kasar Libya sun bukaci firai ministan kasar Abdulhamid Dubba ya sauka saboda shi ne ya haddasa rikicin da ya faru a cikin yan makonnin da suka gabata a kasar.
Shafin yanar gizo na labarai Africa News ya bayyana cewa masu zanga zanga kimani 200 sun taro a tsakiyar birnin Tripoli sun rera takin Dole Dubah ya sauka, wanda kuma suna rera wasu taken.
Tun shekara ta 2011 ne a lokacinda kungiyar tsaro ta nato ta goyi bayan yantawaye suka kashe shugaba Kaddafi ne kasar Libya ta rabu gida biyu, bangaren da MDD ta amince da ita a birnin Tripoli da kuma wacce Khalifa Haftar yake jagoranta daga gabacin kasar.