Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna da Grossi kan sabbin abubuwan da suka shafi tattaunawar nukiliyar Iran

Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi da Darakta Janar na Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya Rafael Grossi sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da suka shafi tattaunawar nukiliya da kuma dage takunkumin da aka kakabawa Iran a wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho.

A yayin tattaunawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan sabon ci gaban da aka samu a shawarwarin nukiliyar da kuma dage takunkumin. Sun kuma tattauna rahoton da hukumar ta IAEA ta fitar kan Iran.

Haka nan kuma yayin da yake ishara da yadda Iran ke ci gaba da ba da hadin kai ga hukumar ta IAEA, da aiwatar da dukkan ayyukan nukiliyar kasar Iran karkashin kulawar hukumar IAEA, da kuma cikin tsarin yarjejeniyar kariya, da rashin karkata ayyukan nukiliya da kayayyaki, ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga babban darektan hukumar ta IAEA da ya fayyace gaskiyar lamarin ta hanyar da za ta hana wasu bangarori yin amfani da wannan cibiya ta kasa da kasa wajen cimma manufofinsu na siyasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Oman ta mika wa Iran takardun shawararin Amurka game da tattaunawar nukiliya

Iran ta tabbatar da cewa ta samu shawarar da Amurka ta gabatar mata daga hannun kasar Oman game da shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya da ake tattaunawa a kai.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa Iran ta samu wani bangare na shawarwarin daga Amurka daga Oman mai shiga tsakani kan batun a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X.

Ya karbi sakon ne daga hannun takwaransa na Oman Badr Albusaidi, wanda ya gudanar da wata gajeriyar ziyara a Tehran.

Saidai ministan harkokin wajen Iran din bai bayyana abinda shawarwarin ke kunshe da ba, amma ya jaddada cewa za a duba su a kuma mayar da amsa wacce ta yi daidai da muradin kasar da kuma hakkokin al’ummar Iran.

Har ila yau, a ranar Asabar, Araghchi ya sake jaddada ‘yancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na inganta sinadarin Uranium don zaman lafiya, yana mai cewa hakki ne na kasa da ba za a iya tattaunawa a kai ba.

Tun a watan Afrilu ne dai Iran da Amurka suka faro tattaunawa a shiga tsakanin kasar Oman a kokarin warware sabanin dake tsakanin bangarorin biyu dama wasu kasashen yammacin duniya kan shirin nukiliyar iran na zaman lafiya.

Kasashen dai na zargin Iran da kokarin mallakar makamman kare dangi batun da Iran ke musantawa tana mai cewa shirinta na lumana ne.

Amurka dai na son Iran ta rage inganta sinadarin uranium din ta zuwa “sifili.” Abinda iran ke cewa ba zai yi wu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa
  • Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Nukiliya : Iran ta gargadi kasashen yamma akan daukar duk wani irin mataki kan ta
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Gargadi Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Da Wasu Kasashe
  • Oman ta mika wa Iran takardun shawararin Amurka game da tattaunawar nukiliya
  • Nukiliya : Tehran ta soki rahoton IAEA da cewa bai da tushe
  • Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed
  • Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana