Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed
Published: 1st, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Kamaru Lejeune Mbella Mbella a jiya Jumma’a, wanda ya je Hong Kong don halartar bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa hukumar shiga tsakani ta kasa da kasa mai lakabin “IOMed” a Turance.
A yayin ganawar, Wang ya nuna jin dadinsa kan yadda kasar Kamaru ta taka rawar gani a shirye-shiryen kafa hukumar ta IOMed, kana ya bayyana fatan ganin Kamaru ta amince da abubuwan da taron ya cimma da wurwuri.
A nasa bangaren, Mbella ya ce, shawarar da kasar Sin ta bayar ta kafa hukumar ta IOMed, ta nuna himma da tasirinta, kuma ta yi daidai da ruhin yarjejeniyar kafuwar MDD. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
A lokacin gudanar da bincike, an samu layin waya guda 21 da takardun rijistar layi guda 29 a wajen Suleiman, wanda ya ce yana harkar rijistar layin ne.
Ya amsa cewa shi ne ya bai wa waɗanda “aka sace” waya da lambar da aka yi amfani da ita wajen neman kuɗin fansa.
Binciken ya nuna cewa waɗannan mutanen suna cikin wani tsari na zamba wanda ake kira da Ponzi.
An kuma gano cewa ɗaya daga cikinsu ya haɗa baki da wanda aka ce an yi garkuwa da shi don su karɓi kuɗi daga sauran abokan harkarsu.
SP Abiodun ya ce bincike ana ci gaba da bincike domin kama sauran waɗanda ke da hannu a lamarin, yayin da aka riga aka gurfanar da waɗanda aka kama a kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp