Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Kamaru Lejeune Mbella Mbella a jiya Jumma’a, wanda ya je Hong Kong don halartar bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa hukumar shiga tsakani ta kasa da kasa mai lakabin “IOMed” a Turance.

A yayin ganawar, Wang ya nuna jin dadinsa kan yadda kasar Kamaru ta taka rawar gani a shirye-shiryen kafa hukumar ta IOMed, kana ya bayyana fatan ganin Kamaru ta amince da abubuwan da taron ya cimma da wurwuri.

A nasa bangaren, Mbella ya ce, shawarar da kasar Sin ta bayar ta kafa hukumar ta IOMed, ta nuna himma da tasirinta, kuma ta yi daidai da ruhin yarjejeniyar kafuwar MDD. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Gargadi Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Da Wasu Kasashe

Iran ta gargadi hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya da wasu kasashe

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’ar kasa da kasa Kazem Gharibabadi, ya gargadi hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA da wasu kasashen duniya kan ci gaba da bin tafarki maras kyau da suka yi a baya, yana mai jaddada cewa Iran za ta dauki natakin da ya dace daidai ayyukan da sauran bangarori suka dauka.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’a na kasa da kasa ya mayar da martani a jiya Lahadi kan rahoton babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya Rafael Grossi kan wasu batutuwan kariya da suka shafi Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Wasu kafafen yada labarai sun wallafa wani bangare na cikakken rahoton da babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa, IAEA, Rafael Grossi, ya gabatar a jiya, wanda aka shirya gabatar da shi ga taron kwamitin gwamnonin dake tafe. Rahoton ya yi iƙirarin cewa yawan sinadarin Uranium da Iran ke da shi ya kai matakin da zai yi kusa da matakin da ake bukata wajen samar da makaman yaƙi kuma ya nuna rashin gamsuwarsa da Iran ke bayarwa duk da haɗin gwiwar da Iran ke yi da hukumar IAEA.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen AES zasu kafa kotun hukunta manyan laifuka ta kungiyar
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Tattauna Darakta-Janar Na Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Gargadi Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Da Wasu Kasashe
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Yankunan Kasar Siriya Tare Da Kafa Wuraren Bincike
  • Isra’ila ta hana tawagar kasashen Larabawa shiga gabar yammacin kogin Jordan
  • Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa
  • Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana
  • An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Hanyar Warware Takaddamar Shirin Makamashin Nukiliyar Iran