Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15
Published: 19th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ba da umurni kan babban shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin karo na 15, inda ya nanata wajibcin tsai da shiri bisa halin da ake ciki, matakin da ya kasance muhimmiyar dabarar jam’iyyar kwaminis ta Sin wato JKS a fannin gudanar da harkokin kasa, kuma fifiko a siyasance na tsarin mulkin gurguzu mai salon musamman na Sin.
Xi ya ce tsai da babban shiri na 15 na da babbar ma’ana ga tabbatar da manyan tsare-tsare da aka tanada a yayin babban taro karo na 20 na JKS, da gaggauta zamanantar da al’ummar Sinawa. Don haka dole ne a samar da shiri bisa halin da ake ciki, bisa tushen demokuradiyya da doka da shari’a, ta yadda al’ummun kasa za su iya cin gajiyar manyan tsare-tsare.
Ban da wannan kuma, an saurari ra’ayin jama’a daga dukkan fannoni, da koyi da dabarun da aka samu a ayyukan yau da kullum, don dunkule ayyukan da za a yi da manufofin da za a dauka, ta yadda za a cimma nasarar aiwatar da shiri mai inganci.
Sin za ta gudanar da shiri na shekaru biyar-biyar na 15 a badi, yanzu kwamitin kolin JKS na rubuta shawarar tsai da shirin. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha
A yau Alhamis ne aka bude bikin baje kolin hada-hadar tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afirka karo na hudu a birnin Changsha fadar mulkin lardin Hunan, taron dake kara jaddada himmar kasar Sin ta fuskar karfafa alaka da nahiyar Afirka, nahiyar dake da mafiya yawan kasashe masu tasowa a duniya baki daya.
Kusan kamfanonin Sin da na kasashen Afirka 4,700, da sama da mahalarta 30,000 ne za su halarci bikin na kwanaki hudu, wanda aka yiwa taken “Sin da Afirka: Tunkarar zamanantarwa tare.” Rahotanni daga mashirya bikin na cewa, kwarya-kwaryar darajar ayyukan hadin gwiwa da aka amincewa sun haura dalar Amurka biliyan 11.
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin bude baje kolin, inda kuma ya yi amannar cewa taron zai samar da karin damammaki ga hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da haifar da kyakkyawan sakamako.
Wang Yi, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya kara da cewa, duk irin sauyin da aka samu a fannin cudanyar sassan kasa da kasa, Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da nahiyar Afirka, za ta samar da kakkarfan tallafi ga ayyukan zamanantar da nahiyar, da kasancewa kawa ta gari, kuma sahihiyar ‘yar uwa ga Afirka kan hanyar nahiyar ta samun ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp