Leadership News Hausa:
2025-08-04@04:27:58 GMT

Bayern Munich Ta Lashe Gasar Bundesliga Ta Bana

Published: 5th, May 2025 GMT

Bayern Munich Ta Lashe Gasar Bundesliga Ta Bana

Ta tabbata ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayern Munich ta lashe gasar Bundesliga ta bana bayan da Bayer Leverkusen ta buga canjaras a wasanta da Freiburg yau Lahadi.

Itama Munich canjaras ta buga a wasanta na ranar Asabar tsakaninta da RB Leipzig inda aka tashi da ci 3-3, amma kuma sakamakon wasan Bayer Leverkusen dake matsayi na biyu ya tabbatarwa Munich nasarar lashe gasar Bundesliga karo na 34 a tarihinta.

Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United Dortmund Ta Doke Bayern Munich A Wasan Hammayya A Gasar Bundesliga

Za a iya cewa kocin ƙungiyar Vincent Kompany, wanda ya karɓi aikin horar da ƙungiyar bayan korar Thomas Tuchel ya shigo da kafar dama, wannan ne karon farko da tsohon Kocin na Burnley zai lashe wata gasa tun bauan fara aikin koci.

Za a baiwa Bayern Munich kofin a wasanta na gaba da zata buga da kungiyar kwallon kafa ta Borrusia Monchengladbach a filin wasa na Allianz Arena dake birnin Munich, inda akwai yiwuwar wannan ce kakar wasa ta karshe ga mataimakin kyaftin din ƙungiyar Thomas Muller.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Bayern Munich

এছাড়াও পড়ুন:

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMA
  • Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?
  • Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya
  • Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
  • ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
  • Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
  • Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya  
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul
  • Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul