Boko Haram ta kashe sojoji huɗu a Yobe
Published: 4th, May 2025 GMT
’Yan ta’addan Boko Haram da suka kai hari kan rundunar soji ta 27 da ke Buni Yadi a jihar Yobe, sun kashe akalla sojoji hudu tare da lalata kayan aiki da dama na soji.
An kai harin ne kafin wayewar garin Asabar, jim kaɗan bayan da Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas ta gana a Damaturu domin tattauna hanyoyin haɗin gwiwa wajen yaki da ta’addanci.
Wani jami’in tsaro ya bayyana cewa maharan sun kai mummunan hari suna harbul kan mai da harbe-harbe.
Hedikwatar sojojin Najeriya ta tabbatar da harin inda ta bayyana cewa sojoji na fafatawa da ISWAP a Buni Gari.
ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe Rashin tsaro: ‘Ba za mu miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba’Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan asarar rayuka ba.
Mazauna garin Buni Yadi, mahaifar Gwamna Mai Mala Buni, sun tsere zuwa wurare masu aminci, kuma sojoji sun rufe babbar hanyar da ta hada Yobe da kudancin Borno.
Wannan harin ya biyo bayan wani irin harin da aka kai makonni biyu da suka gabata a yankin Chalie na Buni Yadi inda aka ce an kashe sojoji uku.
Hare-haren ’yan ta’adda sun karu a yankunan Borno, inda suke kai hari kan kauyuka da sansanonin soji.
Gwamnan Jihar Borno Babagana Zulum da sauran shugabanni sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki mataki, suna masu nuni da cewa wasu ƙananan hukumomi na karkashin ikon Boko Haram tare da nuna damuwa game da shigowar ’yan ta’adda daga kasashe makwabta.
Sun yi kira da a kai farmaki a yankin tafkin Chadi da dajin Sambisa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar
Jami’an kasashen larabawa da na Musulmi sun bukaci daukar kwararan matakai kan Isra’ila bayan harin da ta kai a birnin Doha, inda suka bayyana harin a matsayin “na matsorata, da muggan laifuka.”
Da yake jawabi a gun taron ministocin harkokin wajen kasashen a birnin Doha, Sakatare-Janar na kungiyar kasashen Larabawa Ahmed Aboul Gheit ya ce harin, ha’inci ne da wauta.”
Sakatare-Janar na Kungiyar ya bayyana “cikakken goyon baya” ga Qatar bayan abin da ya kira “cin zarafin Isra’ila”, yana mai jaddada cewa dole ne kasashen duniya su dauki kwakkwaran mataki kan Tel Aviv.
Shi ma da yake jawabi a taron share fagen kasashen musulmin da na Larabawa, firaministan Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani ya yi tir da harin da ya danganta da na “ta’addancin kasa” da kuma keta duk wani yunkuri na shiga tsakani.”
Sheikh Abdulrahman Al Thani ya bukaci kasashen duniya da su daina yin Magana mai tamkar harshen damo, su kuma hukunta Isra’ila saboda “laifin” da ta aikata.
Ya yi wannan jawabi ne a wani taron share fage da aka yi a jajibirin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Musulunci da Qatar ta shirya bayan da Isra’ila ta kai wani hari irinsa na farko kan kasar a kan shugabannin Hamas a Doha. Yau Litinin ne shugabannin kasashen na Larabawa da na Musulmi zasu hadu a birnin Doha domin tattauna batun.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci