Boko Haram ta kashe sojoji huɗu a Yobe
Published: 4th, May 2025 GMT
’Yan ta’addan Boko Haram da suka kai hari kan rundunar soji ta 27 da ke Buni Yadi a jihar Yobe, sun kashe akalla sojoji hudu tare da lalata kayan aiki da dama na soji.
An kai harin ne kafin wayewar garin Asabar, jim kaɗan bayan da Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas ta gana a Damaturu domin tattauna hanyoyin haɗin gwiwa wajen yaki da ta’addanci.
Wani jami’in tsaro ya bayyana cewa maharan sun kai mummunan hari suna harbul kan mai da harbe-harbe.
Hedikwatar sojojin Najeriya ta tabbatar da harin inda ta bayyana cewa sojoji na fafatawa da ISWAP a Buni Gari.
ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe Rashin tsaro: ‘Ba za mu miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba’Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan asarar rayuka ba.
Mazauna garin Buni Yadi, mahaifar Gwamna Mai Mala Buni, sun tsere zuwa wurare masu aminci, kuma sojoji sun rufe babbar hanyar da ta hada Yobe da kudancin Borno.
Wannan harin ya biyo bayan wani irin harin da aka kai makonni biyu da suka gabata a yankin Chalie na Buni Yadi inda aka ce an kashe sojoji uku.
Hare-haren ’yan ta’adda sun karu a yankunan Borno, inda suke kai hari kan kauyuka da sansanonin soji.
Gwamnan Jihar Borno Babagana Zulum da sauran shugabanni sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki mataki, suna masu nuni da cewa wasu ƙananan hukumomi na karkashin ikon Boko Haram tare da nuna damuwa game da shigowar ’yan ta’adda daga kasashe makwabta.
Sun yi kira da a kai farmaki a yankin tafkin Chadi da dajin Sambisa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari
Sarkin yankin Oke Agbe a Jihar Ondo ya ci Musulmi tara, tare da barazanar koran su da kuma haramta yin addinin Musulunci a garinsa bayan da wasu dodanni suka kai hari a wani masallaci da gidan limami.
Aminiya ta samu rahoto cewa, wasu dodanni sun kai hari a masallaci da gidan wani limami, suka lakaɗa wa matansa da ’ya’yansa duka a yankin Oke Agbe, da ke shiyyar Akoko a Ƙaramar Hukumar Akoko ta Arewa a Jihar Ondo Jihar Ondo.
Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC), ta bayyana cewa, “Basaraken yankin ya yi Musulmin tara da aka ci zalinsu tara, saboda sun yi ihu tare da zagin dodannin, maimakon su riƙa yin kuka suna roƙon dodannin.
“Basaraken ya umarci matan limamin su biya tarar awaki tara da tumaki bakwai da kuma ƙwarya biyu na hoto, cikin kwana uku, kafin ranar Litinin da ta gabata, ko kuma a haramta musu zama a garin.”
Ɗan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra Yadda Cin ganyayyaki ke gagarar ’yan NajeriyaShugaban Ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, dodannin sun kai wannan harin ne a ranar Alhamis 12 ga watan Yuni, nan da muke ciki.
Farfesa Ishaq Akintola, ya bayyana harin a matsayin wata shaida da ke nuna yadda ake tsananin cin zarafin Musulmi a yankin Yarabawa, don haka ya kira da a ɗauki matakin shari’a a kan duk masu hannu a wannan aika-aika.
Ya ci gaba da cewa abin da ya faru ya ƙara girman fargabar da ƙungiyar take da shi gane da makomar al’ummar Musulmi a yankin Kudu maso yammacin Najeriya, “saboda abin sai ƙara muni yake ta yi.”
Don haka muna Allah-wadai da wannan hari na jahiliyya, da kuma zaluncin wannan sarki, wanda ya ci karo da kundin tsarin mulkin ƙasa, a ƙarƙashin tsarin dimokuraɗiyya a ƙarni na 21.
“Muna kira da a yi wa waɗannan Musulmi adalci, kuma muna kira ga Gwamnatin Jihar Ondo ya taka wa Sarkin Oke Agbe Akoko bukri, tare da tabbatar da cewa wani abin ƙi bai samu limamin ko ’ya’yansa ko matansa ba. Sa’annan dole a janye maganar haramta musu zama a garin,” in ji kungiyar Musulmin.