Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Sokin Kasar Faransa Kan Mummunar Rawar Da Take Son Takawa Kan Iran
Published: 3rd, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya soki mummunar rawar da Faransa ke takawa
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya soki kasar Faransa saboda abin da ya bayyana a matsayin gurgunta rawar da take takawa a kokarin diflomasiyya kan matsayin Shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
A wani rubutu da ya yi a dandalin X, kakakin ya yi tsokaci kan zargin na Faransa, yana mai cewa: Ikirarin da ministan harkokin wajen Faransa ya yi na cewa Iran na daf da kera makamin nukiliya, da’awa ce ta karya kuma marar tushe.
Ya kara da cewa: Wadannan kalamai na karya, tare da barazanar sake kakabawa Iran takunkumi, suna kara karfafa ra’ayin cewa matsayar Faransa na rikidewa zuwa wani matsayi na barna.
Ya ci gaba da cewa: Irin wannan tsarin ba zai karawa Faransa kwarin gwiwa ko matsayinta a Turai ko duniya ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
Ministan harkokin wajen Omani Badr Albusaidi ya sanar da cewa, ba za a gudanar da zagaye na shida na tattaunawar nukiliya tsakanin Iran da Amurka ba.
Yau Lahadi ne aka shirya gudanar da zagaye na gaba na shawarwari a Muscat babban birnin kasar Oman.
A cikin wani sakon da ya wallafa a kan X (tsohon Twitter), Albusaidi ya tabbatar da sokewar, yayin da ya jaddada cewa “diflomasiyya da tattaunawa sun kasance hanya daya tilo ta samun zaman lafiya mai dorewa.”
“Tattaunawar Iran da Amurka, wadda aka shirya gudanar da ita a birnin Muscat ranar Lahadin nan, ba za ta gudana a yanzu ba.
Tattaunawar diflomasiyyar da aka faro kan shirin nukiliyar Iran, a watan Afrilu a shiga tsakanin masarautar Oman, ta wargaje biyo bayan mummunan harin da Isra’ila ta kai kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugabar harkokin wajen kungiyar EU Kaja Kalas a ranar Asabar, ya ce ci gaba da tattaunawa da Amurka a cikin danyen aikin da Isra’ila ke yi bai da wata fa’ida.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ce kalaman shugaban Amurka sun tabbatar da cewa matakin da Isra’ila ta dauka kan Iran ya samo asali ne daga goyon bayan da Washington ke baiwa gwamnatin Tel-Aviv kai tsaye.