Aminiya:
2025-05-01@18:11:30 GMT

’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa na Bayelsa

Published: 1st, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin ’yan fashi ne sun kai hari kan wani jirgin ruwa da ke jigilar mata ’yan kasuwa zuwa Ƙaramar hukumar Ijaw ta Kudancin Jihar Bayelsa, a kan hanyar ruwan Lobia/Foropa.

Rahotanni sun ce maharan sun yi garkuwa da wasu mata huɗu a lokacin da lamarin ya faru a ranar Talata.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta Najeriya za ta karɓi baƙuncin Gasar Karatun Alkur’ani ta Duniya a karon farko 

Wata majiyar unguwar da lamarin ya faru ta shaida wa Daily Trust a safiyar ranar Alhamis, maharan sun kai harin ne ’yan mintuna kaɗan bayan jirgin ruwan fasinjan ya tashi daga gaɓar ruwan Swali a Yenagoa, babban birnin jihar.

Ya ce, kimanin mutane 12 da ke cikin kwale-kwalen an ƙwace dukiyoyinsu da kuɗaɗensu, yayin da ’yan fashin suka yi awon gaba da huɗu daga cikin matan zuwa cikin daji ba tare da sanin dalilansu ba.

A halin yanzu, Ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Ijaw ta kudu ta 4 a majalisar dokokin Jihar Bayelsa kuma shugaban kwamitin kare haƙƙin ɗan Adam na majalisar Honorabul Selekaye Victor-Ben, ya yi Allah wadai da lamarin.

Ya kuma bayyana sace mutanen a matsayin harin da aka kai wa waɗanda ba su ji ba ba su gani ba.

A cewarsa, “Ba wai cin mutuncin bil’adama ba ne kawai, har ma da babbar barazana ga zaman lafiya da tattalin arzikin mazaɓarmu da ma jihar baki ɗaya.

“Ina yin Allah wadai da wannan ta’addanci da kakkausar murya kuma ina bayar da haɗin kai tare da iyalan waɗanda abin ya shafa a wannan lokaci mai tsanani.”

Ya kuma yi kira ga gwamnatin Jihar Bayelsa da dukkanin hukumomin tsaro da abin ya shafa, musamman rundunar ’yan sandan Najeriya da su gaggauta sakin waɗannan matan da aka sace ba tare da wani sharaɗi ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashin teku Bayelsa Ijaw

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike

Rahotonni sun tabbatar da cewa: Da tsakar daren jiya Litinin wayewar garin yau Talata, sojojin mamayar Isra’ila dauke da motocin soji guda hudu da wasu sojoji masu tafiyar kafa sun kutsa cikin yankunan kasar Siriya daga titin Al-Hurriya, inda suka wuce titin Al-Kassarat, zuwa Talat Jabata Al-Khashab.

Majiyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Siriya ta bayyana cewa: Sojojin mayar sun kafa shingen binciken ababen hawa inda suka tsaya suna binciken ababan hawa da ke wucewa, sannan suka haska wuta don gano hanyar kafin su fita ta hanyar da suka shiga. Jiragen saman yakin haramtacciyar kasar Isra’ila kuma suna shawagi a sararin samaniyar birnin Damascus fadar mulkin kasar ta Siriya.

A jiya Litinin ma, sojojin mamayar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a wasu sansanoni na rundunar sojin ta 36 ta musamman da aka fi sani da Ain al-Burj a gabashin kauyen Qala’at Jandal da ke cikin karkarar birnin Damascus, tare da kafa wani sansanin soji a saman dutsen Barbar domin sa ido kan motsin da ake yi a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Raba Rigunan Kariya Ga Wasu Jihohin Najeriya.
  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike