Aminiya:
2025-07-31@17:52:05 GMT

’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa na Bayelsa

Published: 1st, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin ’yan fashi ne sun kai hari kan wani jirgin ruwa da ke jigilar mata ’yan kasuwa zuwa Ƙaramar hukumar Ijaw ta Kudancin Jihar Bayelsa, a kan hanyar ruwan Lobia/Foropa.

Rahotanni sun ce maharan sun yi garkuwa da wasu mata huɗu a lokacin da lamarin ya faru a ranar Talata.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta Najeriya za ta karɓi baƙuncin Gasar Karatun Alkur’ani ta Duniya a karon farko 

Wata majiyar unguwar da lamarin ya faru ta shaida wa Daily Trust a safiyar ranar Alhamis, maharan sun kai harin ne ’yan mintuna kaɗan bayan jirgin ruwan fasinjan ya tashi daga gaɓar ruwan Swali a Yenagoa, babban birnin jihar.

Ya ce, kimanin mutane 12 da ke cikin kwale-kwalen an ƙwace dukiyoyinsu da kuɗaɗensu, yayin da ’yan fashin suka yi awon gaba da huɗu daga cikin matan zuwa cikin daji ba tare da sanin dalilansu ba.

A halin yanzu, Ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Ijaw ta kudu ta 4 a majalisar dokokin Jihar Bayelsa kuma shugaban kwamitin kare haƙƙin ɗan Adam na majalisar Honorabul Selekaye Victor-Ben, ya yi Allah wadai da lamarin.

Ya kuma bayyana sace mutanen a matsayin harin da aka kai wa waɗanda ba su ji ba ba su gani ba.

A cewarsa, “Ba wai cin mutuncin bil’adama ba ne kawai, har ma da babbar barazana ga zaman lafiya da tattalin arzikin mazaɓarmu da ma jihar baki ɗaya.

“Ina yin Allah wadai da wannan ta’addanci da kakkausar murya kuma ina bayar da haɗin kai tare da iyalan waɗanda abin ya shafa a wannan lokaci mai tsanani.”

Ya kuma yi kira ga gwamnatin Jihar Bayelsa da dukkanin hukumomin tsaro da abin ya shafa, musamman rundunar ’yan sandan Najeriya da su gaggauta sakin waɗannan matan da aka sace ba tare da wani sharaɗi ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashin teku Bayelsa Ijaw

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da zagayen farko na makon lafiyar mata da jarirai da jarirai (MNCHW) na shekarar 2025 tare da raba fakiti 6,000 na kayan haihuwa da na’urar (C/S) 500 ga cibiyoyin lafiya a fadin jihar.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya wakilta shi ne ya jagoranci bikin kaddamar da shirin a hukumance da aka gudanar a cibiyar lafiya matakin farko na Birji da ke karamar hukumar Madobi.

 

Ya yi nuni da cewa, wannan aikin ya hada da na rigakafi na yau da kullun ga yara, karin sinadarin Vitamin A, Rarraba gidajen sauro masu maganin kwari ga mata masu juna biyu.

 

Gwamna Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na karfafa wa shirin rabon gidajen sauro ta hanyar ware naira miliyan 140 domin adana gidajen sauro da aka raba.

 

Gwamnan ya bukaci mata da masu kulawa da su yi amfani da damar da za a yi na tsawon mako guda don samun muhimman ayyukan kiwon lafiya da ake bayarwa kyauta.

 

A cikin sakon sa na fatan alheri, shugabar ofishin UNICEF a Kano, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta kara yawan kwanakin hutun haihuwa da ake biyarwa domin kare lafiyar mata da jarirai da kuma inganta shayar da jarirai nonon uwa zalla.

 

Taron ya samu halartar kwamishinan lafiya, shugaban karamar hukumar Madobi, Hakimin Shanono, abokan cigaba, masu rike da mukaman siyasa da duk masu ruwa da tsaki.

 

 

COV/Khadija Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14