HausaTv:
2025-05-01@14:10:21 GMT

Amurka Ta Kakabawa Kamfanonin Da Suka Hulda Da Iran Bangaren Man Fetur

Published: 1st, May 2025 GMT

A dai-dai lokacin da kasashen Amurka da JMI suke ci gaba da tattaunawa kan shirin makamashin nukliya ta Iran gwamnatin Amurka a jiya Laraba ta dorawa kamfanoni da mutanen da suke mu’amala da JMI a bangaren man Fetur takunkuman tattalin arziki. Da dama daga cikin wadannan kamfanoni na kasar China ne.

Jaridar ‘the Nation’ ta Amurka ta ce tun farkon wannan shekarar ne shugaban Trump ta farfado da takurawar tattalin arziki  mafi muni a ka kasar Iran da nufin tilasta mata dawowa teburin tattaunawa ko kuma ta wagaza cibiyoyin Nukliyar kasar.

A halin yanzu dai kasashen biyu zasu ci gaba da tattaunawar ba kai tsaye ba,  karo na hudu a birnin Roma na kasar Italiya a ranar Asabr mai zuwa. Kuma mai yuwa daga karshe su samarda sabuwar yarjeniya a tsakaninsu, kuma akwai yiuwar su kasa yin haka.

Wannan kuma zai faru ne idan Amurka ta bukaci JMI ta daina mu’amala da sinadarin Uranium kwatakwata ko kuma ta shigar da wata bukata wacce Iran ba zata amince ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra

A wani taro wanda ya hada ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI da kuma mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara, bangarorin biyu sun tabbatar da cewa an kammala aikin shimfida layin dogo tsakanin garin Shalamcheh na kasar Iran da kuma birnin Basra a kasar Iraki.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jami’an gwamnatocin kasashen biyu na fadar haka, sun kuma jaddada muhimmancin layin dogon da kuma samar da kasuwar babu kudaden fito a kan iyakokin kasashen biyu.

Labarin ya kara da cewa harkokin kasuwanci tsakanin kasashen biyu ya zuwa yanzu ya kai dalar Amurka biliyon $11a ko wace shekara kuma anan saran nan gaba zai iyakaruwa zuwa dalar Amurka biliyon $25.

Rahmatollah Akrami, ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI, da kuma Hazem Majid Naji Al-Khalidi mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara sun jaddada muhimmancin kammala layin dogo tsakanin kasashen biyu, da kuma kasuwar ba kudaden fito tsakanin kasashen biyu. Da kuma fatan zasu yi kokarin amfanar juna gwagwadon abinda zasu iya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tace Samar Da Kasar Falasdinu Mai Cikekken Yenci Ba Abin Tattaunawa Bane
  • Arif: A Shirye Muke Mu Sabunta Sana’o’in Sudan
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba