Kasashen Masar da Kuwaiti sun fitar da sanarwa a yau Litinin ta yin tir da kiraye-kirayen da wasu yahudawa masu tsattsauran ra’ayi suke yi domin a rusa masallacin kudus, suna masu yin kira ga kungiyoyin kasa da kasa domi a tsayar da tsokanar da Isra’ilawa suke yi.

Kasashen biyu dai sun fitar da wannan sanarwar ne bayan da wasu yahudawa su ka watsa wani faifen bidiyo na tarwatsa masallacin Kudus da kuma maye gurbinsa da gina wajen bautar yahudawa.

Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta bayyana cewa: “Jamhuriyar Larabawa ta Masar tana yin tir da kakkausar murya akan kiraye-kirayen da masu tsattsauran ra’ayin ‘yan share wuri zauna suke yi na tarwatsa masallacin Kudus.

Haka nan kuma Masar din ta yi kira da a kawo karshen keta hurumin masallacin Kudus wanda yake tsokana ce ga al’ummar musulmi.

Ita ma kasar Kuwaiti ta fitar da bayani da a cikin ta yi tir da kora zuwa ga rusa masallacin Kudus da kungiyoyin ‘yan share wuri zauna suke yi. Ta kuma kara da cewa, kiraye-kiraye irin wadannan tsokana ce ga al’ummar musulmin duniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kiraye kiraye

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran

A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”

Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan  mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.

A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo