Kasashen Masar da Kuwaiti sun fitar da sanarwa a yau Litinin ta yin tir da kiraye-kirayen da wasu yahudawa masu tsattsauran ra’ayi suke yi domin a rusa masallacin kudus, suna masu yin kira ga kungiyoyin kasa da kasa domi a tsayar da tsokanar da Isra’ilawa suke yi.

Kasashen biyu dai sun fitar da wannan sanarwar ne bayan da wasu yahudawa su ka watsa wani faifen bidiyo na tarwatsa masallacin Kudus da kuma maye gurbinsa da gina wajen bautar yahudawa.

Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta bayyana cewa: “Jamhuriyar Larabawa ta Masar tana yin tir da kakkausar murya akan kiraye-kirayen da masu tsattsauran ra’ayin ‘yan share wuri zauna suke yi na tarwatsa masallacin Kudus.

Haka nan kuma Masar din ta yi kira da a kawo karshen keta hurumin masallacin Kudus wanda yake tsokana ce ga al’ummar musulmi.

Ita ma kasar Kuwaiti ta fitar da bayani da a cikin ta yi tir da kora zuwa ga rusa masallacin Kudus da kungiyoyin ‘yan share wuri zauna suke yi. Ta kuma kara da cewa, kiraye-kiraye irin wadannan tsokana ce ga al’ummar musulmin duniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kiraye kiraye

এছাড়াও পড়ুন:

Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres

Babban Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres,ya bayyana cewa, samar da makamashi mai tsabta da zai daidaita tsarin rayuwar dan Adam daga sarrafa wuta, ta hanyar yin amfani da tururi, zuwa rarrabuwar ma’adinan, shi ne ginshikin bunkasar al’umma.

Mista Gutterres ya bayyana hakan ne a taron inganta samar da makamshi da aka gudanar a harabar ofishin Majalisar Dinkin Duniya.

Ya ce “a yau, muna son tabbatar da yadda za a farka bisa tsarin sabon zamani. Rana tana fitowa don samar da makamashi mai tsabta ga al’umma.

A bara, kusan dukkanin sabbin qarfin wutar lantarki sun fito ne daga abubuwan da ake sabuntawa.

Zuba jari a harkar samar da makamashi mai tsafta darajarsa ta haura zuwa Dala tiriliyan 2 – Dala biliyan 800 fiye da abin da ake samu daga albarkatun mai.

Hasken rana da iska yanzu su ne hanyoyin samar da wutar lantarki mafi arha a duniya, kuma sassan makamashi masu inganci da suke samar da ayyukan yi, kuma suna kara habaka da ci gaba.

Kasashen da ke tattare da burbushin dake samar da makamashi ba sa iya kare tattalin arzikinsu, suna yi musu zagon kasa wanda ke haifar musu rasa wata babbar dama ta tattalin arziki a karni na 21.

Samar da tsabtataccen makamashi yana ba da damar ikon mallakar duk wani nau’i a fannin makamashi da tsaro.

Kasuwannin man fetur ya kasance daga cikin abubuwan yasa farashin da kuma gazawar samar da kayayyaki da rikice-rikice kamar yadda muka gani lokacin da Rasha ta mamaye Ukraine.

Amma sam duk da hauhawar farashin man fetur, farashin hasken rana, da bashi da takunkumin yana samar da iska, ga kusan kowace al’umma.

A karshe, tsabtataccen makamashi yana havaka, wanda hakan zai iya kai wa ɗaruruwan miliyoyin mutanen dake rayuwa ba tare da wutar lantarki ba a cikin sauri da araha, musamman ta hanyar dakile wutar lantarki da fasahar hasken rana.

Ana barin kasashe masu tasowa a baya. Har ila yau dai makamashin ya mamaye tsarin, kuma har yanzu hayakin yana karuwa lokacin da gaza aiki don gujewa faxawa rikicin sauyin yanayi. Don gyara wannan, muna buƙatar aiki domin daukar mataki.

Na farko, dole ne gwamnatoci su ba da himma wajen samar da tsaftataccen makamashi a nan gaba. A cikin watanni masu zuwa, kowace ƙasa ta yi alƙawarin gabatar da sabbin tsare-tsare na yanayi na ƙasa. Tare da manufa ta shekaru goma masu zuwa. Dole ne wadannan tsare-tsare su kasance sunyi daidaito tare da ƙayyadaddun yanayin zafi a duniya zuwa ma’aunin Celsius 1.5. Kasashen G20, wadanda ke da alhakin kusan kashi 80% na hayakin duniya, dole ne su jagoranci hakan.

Na biyu, dole ne mu gina tsarin makamashi na karni na 21. Ba tare da wata tangarda ta zamani ba, ƙarfin sabunta tsarin yanayi zai iya cika wannan buri namu. Amma ga kowace Dala da aka saka a cikin harkar wutar lantarki.

Na uku, dole ne gwamnatoci su kudiri aniyyar tabbatar da biyan buƙatun makamashi na duniya tare da sabuntawa. Dole ne manyan kamfanonin fasaha suma su taka rawarsu.

Zuwa shekarar 2030, cibiyoyin bayanai za su iya cinye wutar lantarki mai yawa kamar yadda Japan ke yi a yau. Kamfanoni ya kamata su himmatu wajen ba da iko tare da sabuntawa.

Na hudu, dole ne mu sanya adalci a cikin samar da canjin makamashi. Wannan yana nufin cewa tallafa wa al’ummomin da ke dogaro da albarkatun mai don shirya ingantaccen makamashi a nan gaba. Kuma yana nufin sake fasalin samar da ma’adanai mai muhimmanci.
Na biyar, dole ne mu tabbatar da an tsarin samar da makamashi.

Tsabtace hanyoyin samar da makamashi na da matuƙar tasiri wajen mayar da hankali sosai kuma kasuwancin duniya zai bunkasa.

Kasashen da suka kuduri aniyar samar da makamashi dole ne su yi aiki don rarraba kayayyaki, da rage haraji kan kayayyakin makamashi da kuma sabunta yarjejeniyar saka hannun jari ta yadda za su goyi bayan sauyin.

Na shida kuma na karshe, dole ne mu fitar da kudi zuwa ga qasashe masu tasowa. Afirka ta samu kashi biyu ne kacal na jarin da za a iya sabuntawa a bara, duk da cewa tana da kashi 60% na mafi kyawun albarkatun hasken rana a duniya.

Muna buƙatar matakan kasa da kasa don hana biyan basussuka da ake tsotsewa daga kasafin kudin wadannan ƙasashe masu tasowa da kuma ba da dama ga bankunan wajen ci gaban bunkasa ƙasashe da yawa su haɓaka ƙarfin ba da lamuni, da yin amfani da kuɗi masu zaman kansu sosai.

Muna kuma buƙatar hukumomin masu saka hannun jari da su yi la’akari da alƙawarin samar da makamashi mai tsafta.

Wani sabon yanayi na makamashi yana kusa da kai wa ga samun nasara, kuma zai zama da arha, sannan ya kasance wadataccen makamashi mai tsabta da zai samarwa duniya makamshi wadatacce, wajen bunkasa tattalin arziki, kasashe na ‘yancin cin gashin kai da kuma bayar da wutar lantarki kyauta ga kowa.

A nan lokacinmu ne da za mu iya ɗaukar nauyin sauyin duniya. Mu kuma yi amfani da shi yadda ya kamata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  •  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza