Aminiya:
2025-07-31@01:00:38 GMT

PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike

Published: 18th, April 2025 GMT

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce babbar jam’iyyar adawa ta PDP ba ta da wani kyakkyawan tsari da za ta iya kayar da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen 2027.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai kai tsaye a Abuja ranar Juma’a.

Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno

Daily Trust ta ruwaito cewa, shugabannin adawa a faɗin ƙasar nan na ƙara zage damtse wajen ganin sun ƙulla alaƙa da nufin kawar da Jam’iyyar APC.

Sai dai kuma, mabambantan buƙatu tsakanin manyan masu ruwa da tsaki na ci gaba da kawo cikas ga ci gaban tattaunawar ƙawancen da suke yi.

Da yake bayani a yayin taron manema labarai, Wike ya ce: “PDP ba ta shirya zaɓen 2027 ba, a bayyane yake, misali ina da jarrabawa kuma zan je aji don karatu, shin ina yin karatun? Ina fahimtar karatun? Ba ka buƙatar ka yaudari wani da cewa kana karatu. Kana ƙoƙarin zuwa karatun ne kawai don mutane su ga cewa ka ɗauki jakarka zuwa aji.

“Halin da PDP ke ciki ke nan, don haka ba za su iya cewa tabbas sun shirya wa zaɓen 2027 ba, gwagwarmayar neman mulki ba za ta iya taimakawa jam’iyyar ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban Birnin Tarayya FCT Nigeriya zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Iran Da Rasha                                                                                                                       

Mai ba da shawara ga Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya bayyana cewa: Hanyar Zangezur wata shiri ne na Amurka don matsawa kasashen Rasha da Iran.

Ali Akbar Velayati mai ba wa Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran shawara kan harkokin kasa da kasa, ya dauki aikin Zangezur (arewa maso yammacin Iran) a matsayin wani aikin Amurka na matsawa kasashen Rasha da Iran lamba.

A cikin wani sako na tunawa da Sheikh Safi al-Din Ardebili, Velayati ya yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi Azarbaijan da mashigar Zangezur, yana mai cewa, “Makiya Iran karkashin jagorancin ‘yan sahayoniyyan duniya da Amurka, suna neman ta hanyar tsare-tsare irin su mashigar Zangezur, don ciyar da manyan ayyukan siyasa a karkashin fakewa da wadannan tsare-tsare.”

Ya kara da cewa, manufar farko ita ce raunana gwagwarmaya da yanke  alakar Iran da yankin Caucasus da kuma killace Iran da Rasha ta kasa a kudancin yankin.

Ya bayyana cewa: “Wannan aikin ba wai kawai wani bangare ne na shirin Amurka na maye gurbin Ukraine da yankin Caucasus a matsayin wani sabon fage na matsin lamba kan Rasha da Iran ba, amma ana aiwatar da shi ne tare da goyon bayan kungiyar tsaro ta NATO da kuma wasu kungiyoyin ‘yan kishin kasa na Turkiyya (Pan-Turkist).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa
  • SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
  • Arewa za ta kayar da Tinubu a zaɓen 2027 —Babachir
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Iran Da Rasha                                                                                                                       
  • Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo