PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike
Published: 18th, April 2025 GMT
Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce babbar jam’iyyar adawa ta PDP ba ta da wani kyakkyawan tsari da za ta iya kayar da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen 2027.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai kai tsaye a Abuja ranar Juma’a.
Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia An kashe sojoji, fararen hula da dama a BornoDaily Trust ta ruwaito cewa, shugabannin adawa a faɗin ƙasar nan na ƙara zage damtse wajen ganin sun ƙulla alaƙa da nufin kawar da Jam’iyyar APC.
Sai dai kuma, mabambantan buƙatu tsakanin manyan masu ruwa da tsaki na ci gaba da kawo cikas ga ci gaban tattaunawar ƙawancen da suke yi.
Da yake bayani a yayin taron manema labarai, Wike ya ce: “PDP ba ta shirya zaɓen 2027 ba, a bayyane yake, misali ina da jarrabawa kuma zan je aji don karatu, shin ina yin karatun? Ina fahimtar karatun? Ba ka buƙatar ka yaudari wani da cewa kana karatu. Kana ƙoƙarin zuwa karatun ne kawai don mutane su ga cewa ka ɗauki jakarka zuwa aji.
“Halin da PDP ke ciki ke nan, don haka ba za su iya cewa tabbas sun shirya wa zaɓen 2027 ba, gwagwarmayar neman mulki ba za ta iya taimakawa jam’iyyar ba.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babban Birnin Tarayya FCT Nigeriya zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cikakken shirin Iran na tunkarar duk wani mataki na wuce gona da iri a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar barazanar daukar matakin soji kan kasar.
Manjo Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne yau Alhamis, yayin da rahotanni ke nuni da cewa, Amurka ta sanya ofisoshin jakadancinta da sansanonin sojinta da ke yammacin Asiya cikin shirin ko-ta-kwana saboda fargabar yiwuwar kai wa Iran hari.
“A wasu lokuta makiya suna yi mana barazana da daukar matakin soji, mun sha bayyanawa, kuma muna maimaitawa a yau, cewa mun shirya tsaf don fuskantar duk wani yanayi,” in ji shi.
“Muna da kwarewa, mun karfafa karfinmu tare da samar da dabaru a cikin tsare-tsarenmu.
Muna sa ido sosai kan sojojin abokan gaba kuma mun aiwatar da shirye-shiryenmu.” Inji shi.
Har ila yau babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya gargadi makiya game da duk wani gigi, ya kuma shawarce su da su yi la’akari da illolin da ayyukansu zasu haifar.