Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
Published: 18th, April 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Benuwe a ranar Alhamis ta tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali a unguwar Otobi da ke Ƙaramar hukumar Otukpo biyo bayan wani mummunan hari da ya tilastawa mazauna garin barin gidajensu.
Kakakin rundunar ’yan sandan, CSP Catherine Anene a wata tattaunawa ta wayar tarho da wakiliyarmu, ta kuma yi watsi da rahoton sabbin hare-haren da aka kai kan unguwannin Emichi, Okpomaju da Odudaje, inda ta bayyana su a matsayin rahoton ƙarya don yawo tsoratar da jama’a.
“Unguwar Otobi yanzu akwai kwanciyar hankali, mun bar wasu jami’anmu tun ranar Laraba ana gudanar da bincike,” in ji Anene.
A halin da ake ciki, Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia ya bayyana cewa har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyen ba bayan harin.
“Mun yi asarar mutane 11. Mun tura ƙarin jami’an tsaro,” in ji gwamnan yayin wani taron manema labarai inda ya bayyana hare-haren a matsayin batun ƙwace fili.”
Da yake mayar da martani kan wannan ci gaban, Sanata mai wakiltar mazaɓar Benuwe ta Kudu kuma shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawa, Abba Moro ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta ci gaba da gazawa wajen kare rayuka, al’ummarsa za su iya amfani da hanyoyin kare kansu.
Sanatan, a cikin wata sanarwa da Emmanuel Eche’Ofun John, mashawarcinsa kan harkokin yaɗa labarai ya fitar, ya bayyana cewa hare-haren da suka janyo asarar rayuka da dukiyoyi na biliyoyin Naira abu ne da ba za a amince da su ba.
Ya kuma yi kira ga gwamnatoci a kowane mataki da su tashi tsaye wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya kuma yabawa Gwamna Alia da a ƙarshe ya fito ya yi Allah-wadai da wannan aika-aika a jihar, ya kuma buƙace shi da ya ƙara yi wa al’umma aiki, yana mai jaddada cewa ƙoƙarin gwamnati a dukkan matakai bai isa ba.
Moro ya kuma yi kira da a kafa sansanonin hukumomin tsaro a cikin unguwannin jama’a masu rauni
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnan Jihar Benuwe Hyacinth Alia y
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da shirin tallafi guda biyu da suka kai fiye da naira miliyan 392, ga membobin kungiyar direbobi ta NURTW da kuma ƴan kungiyar mahauta a jihar Jigawa.
Wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar masu sana’o’in da ke taka muhimmiyar rawa a rayuwar yau da kullum.
A wajen kaddamar da shirin a filin wasa na Dutse, Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin yana da manufa ta musamman domin tallafa wa jama’a kai tsaye. Ya ce ƙungiyoyin NURTW da mahauta suna da matuƙar tasiri, ba kawai ga membobinsu ba, har ma da al’umma gaba ɗaya, shi ya sa gwamnatinsa ta ga dacewar tallafa musu.
Gwamnan ya kara da cewa taimakon da aka bai wa waɗannan ƙungiyoyi zai kara habaka tattalin arzikin al’ummar jihar. Ya yabawa ƙungiyoyin bisa yadda suka tsaya tsayin daka wajen kare muradun membobinsu.
Ya bukaci shugabannin ƙungiyar da su tabbatar da sa ido sosai da kuma ganin cewa an bi dukkan sharuddan shirin. “Hakan zai tabbatar da cewa motocin sun yi aiki daidai da manufa, tare da bai wa shirin damar dorewa da kuma faɗaɗawa don amfanar da wasu a nan gaba’. In ji shi.
Gwamnan ya yaba da rawar da NURTW ke takawa a tattalin arzikin jihar, yana mai bayyana su a matsayin muhimmin ɓangare na samar da kayayyaki, ko a fannin noma, masana’antu ko kasuwanci. Ya ce babu wata harkar rarraba kaya da za ta yi tasiri ba tare da haɗin guiwar NURTW ba.
A cewarsa, gwamnatinsa na saka jari mai yawa a fannin gina hanyoyin mota, inda aka kammala ayyukan hanya guda 26 da aka gada, da kudin da ya kai sama da naira biliyan 100. Haka kuma, an ƙara bayar da kwangiloli don gina tituna 50 masu tsawon fiye da kilomita 850, da kudinsu ya haura naira biliyan 300.
Gwamnan ya bayyana cewa an fara amfani da hanyoyin makamashi masu tsafta, inda aka kusa kammala cibiyar sauya motoci zuwa CNG a jihar. Ya ce wannan cibiya za ta taimaka matuƙa wajen rage farashi da kuma tsaftace muhalli, tare da fa’ida kai tsaye ga ƴan NURTW.
A wani ɓangare na shirin, Gwamna Namadi ya kaddamar da tsarin lamuni na naira miliyan 113 ga ƴan kungiyar mahauta. Shirin zai taimaka wa mutane 53, inda manyan ‘yan kasuwar dabbobi 15 za su samu naira miliyan 5 kowanne, sai sauran 38 da za su samu miliyan 1 kowanne.
Ya ce ana sa ran wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar kiwon dabbobi da samar da nama a jihar, har da kasuwannin nama gaba ɗaya.
Don tabbatar da dorewar wannan ci gaba, gwamnan ya bayyana shirin kafa sabuwar ma’aikatar ci gaban kiwo a jihar.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa a matakin farko na shirin, an raba motoci 36 na kasuwanci da darajarsu ta kai naira miliyan 279.3, tare da inshora, ga membobin NURTW karkashin tsarin lamuni na juyi da hukumar Youth Economic Empowerment da Employment ta jihar ke jagoranta.
Usman Muhammad Zaria