Cin Zali Ba Zai Iya Hana Kasashen Afirka Ci Gaba Ba
Published: 7th, April 2025 GMT
A nata bangare, ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ita ma ta sanar da cewa, kowace kasa na da hakkin neman ci gaba, saboda haka bai kamata a ba wasu kasashe damar yin babakere ba. Ganin yadda kasar Amurka ke neman dora moriyarta a kan hakkin kasashen duniya, ya sa kasar Sin kin amincewa da matakinta.
Yanzu haka ra’ayin kasar Sin na samun amincewa daga mutanen kasashe daban daban. Bisa sakamakon binciken ra’ayin jama’a da kafar watsa labarai ta kasar Sin CGTN ta gudanar, cikin mutanen kasashe daban daban da aka yi musu tambayoyi, kaso 86.9% sun ce matakan ramuwar gayya da kasashe daban daban suka dauka bisa matakin karbar karin haraji na kasar Amurka, sun halatta, kana kaso 87.7% na mutanen sun ce ya kamata kasashe daban daban su yi hadin gwiwa, a kokarin dakile matakin Amurka na cin zarafin sauran kasashe.
A nahiyar Afirka ma, matakin Amurka ya janyo sabon tunani kan dabarar raya kasa. Inda masanin ilimin shari’a na kasar Najeriya Livingstone Wechie ya ce, ko da yake kasar Amurka ta taba alkawarin raya masana’antu a kasashen Afirka karkashin dokar AGOA, sakamako na karshe ya nuna cewa ta yi karya ke nan. Saboda haka mista Wechie ya ce dogara kan tallafin da ake samu daga kasashen waje ba zai raya tattalin arzikin kasashen Afirka yadda suke bukata ba.
Kana a ganin masaniyar ilimin tattalin arziki ‘yar kasar Afirka ta Kudu, Annabel Bishop, cin zalin da kasar Amurka ke yi, zai sa kasashen Afirka gaggauta karkata ga abokan hulda dake kan hanyar tasowa wajen gudanar da ciniki.
Ban da haka, Leseko Makhetha, masanin ilimin tattalin arziki na kasar Lesotho, ya ce matsin lambar da kasar Amurka ta yi wa kasashen Afirka, za ta sa su kara kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka.
Yayin da a nata bangare, minista mai kula da masana’antu, ciniki da zuba jari ta kasar Najeriya, Jumoke Oduwole, ta ce matakin matsin lamba na Amurka ya sa Najeriya tabbatar da niyyar raya bangaren fitar da kayayyakin da ba su shafi danyen mai ba. A cewarta, Najeriya za ta yi kokarin inganta kayayyakinta, don neman sayar da su a karin kasuwannin kasashe daban daban.
Amurka na son toshe hanyar neman ci gaban tattalin arziki ta kasashen Afirka, da ta sauran kasashe masu tasowa na nahiyoyi daban daban. Sai dai ba za ta samu biyan bukata ba. Saboda matakin cin zalin ba zai haifar da komai ba, illa farkarwa, da dogaro da kai, da karfin zuci, da hadin kai, ga kasashe daban daban. Tabbas rinjayen kasashe, wadanda suke da adalci, za su ci nasara a karshe, a wannan gasar da ake gudanar da ita a duniya. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi kakkausar suka ga harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, inda ta bukaci kasashen Larabawa da na musulmi da su dauki matsaya daya kan matakan wuce gona da iri na gwamnatin mamayar.
Basem Naim, mamba a ofishin siyasa na kungiyar Hamas,ne ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, yayin da ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da na kasashen musulmi suka halarci taron gaggawa na Doha, domin tattauna harin da Isra’ila ta kai kan shugabannin Hamas a kasar Qatar.
Babban jami’in na Hamas ya yi kira ga shugabannin yankin da ke halartar taron da su mayar da Isra’ila saniyar ware a siyasance da ta fuskar tattalin arziki da kuma gurfanar da jami’an Isra’ila a kotunan duniya domin kawo karshen yakin kisan kare dangi a Gaza.
Naim ya kuma jaddada cewa, harin da Isra’ila ta kai kan tawagar Hamas a birnin Doha, ya zo ne a daidai lokacin da tawagar ke tantance wata sabuwar shawarar tsagaita bude wuta a Gaza.
“Mun nuna sassauci mafi girma na kawo karshen kisan kiyashin da ake yi a Gaza, amma sojojin mamaya ne, ta hanyar amfani da kisa da kuma sanya sharuddan nasu, ke kawo cikas ga duk wata yarjejeniya da za a iya cimma.”
Daga karshe ya bayyana cewa kungiyar Hamas tana sa ran taron zai dauki matsaya guda daya mai ma’ana tsakanin Larabawa da musulmi, da suka hada da tsagaita bude wuta nan take da kawo karshen yakin Gaza, da dage shingen da aka yi, da yanke duk wata alaka da Isra’ila, da gurfanar da isra’ila kan laifuffukan da ta aikata, da samar da falasdinu mai ‘yancin cin gashin kai, da Al-Quds a matsayin babban birninta, da kuma tabbatar da ‘yancin komawar ‘yan gudun hijira.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bayyana Rashin Halarta Tawagarta A Kada Kuri’a Kan Batun Falasdinu September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci