Aminiya:
2025-11-02@20:54:37 GMT

Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya

Published: 28th, March 2025 GMT

Kisan wasu matafiya ’yan Arewa da aka yi a garin Uromi da ke Ƙaramar Hukumar Arewa maso Gabashin Esan ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya.

A bayan nan ne wasu hotunan bidiyo da aka yaɗa a shafukan sada zumunta suka nuna wasu mutane ɗauke da makamai suna far wa matafiyan da suka taso daga Kudanci zuwa Arewacin Nijeriya.

Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand

Hotunan bidiyon sun nuna yadda aka yi wa waɗanda abin ya shafa jina-jina sannan aka cinna musu wuta suka ƙone ƙurmus.

Tuni dai gwamnatin Edo ta yi Allah wadai da lamarin wanda ya faru a ranar Alhamis tare da ba da umarnin ƙaddamar da bincike a kai.

Wata sanarwa da Sakataren Labarai na Fadar Gwamnatin Edo, Fred Itua ya fitar, ta tabbatar da cewa ’yan sa- kai ne suka kai harin

Sanarwar ta ambato Gwamna Monday Okpebholoce na shan alwashin hukunta “masu laifin.”

“Binciken farko-farko ya nuna cewa matafiya ne da suka taso daga Fatakwal na Jihar Ribas suka ratso ta garin, sai ’yan banga suka kama su da tunanin cewa ɓatagri ne,” kamar yadda Fred Itua ya bayyana.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana adadin mutanen da aka kashe ba a harin, amma ta ce Gwamna Okpebholo ya ziyarci garin a ranar Juma’a, inda ya yi alƙawarin gano waɗanda suke da hannu domin su fuskanci hukunci.

Yayin ziyarar da ya kai wurin da lamarin ya faru, Gwamna Okpebholo ya yaba wa shugabannin ’yan arewacin Nijeriya “bisa yadda suka kwantar da al’amarin cikin hikima” in ji sanarwar.

Mutum 16 aka kashe ’yan asalin Jihar Kano — Amnesty

Ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta ce mutane 16 aka kashe kuma ’yan asalin Jihar Kano ne.

“’Yan sa-kai sun tare matafiyan, suka fito da su daga motarsu, suka yi musu duka, sannan suka cinna musu wuta,” a cewar wani saƙo da Amnesty ta wallafa a shafukan sada zumunta.

Ta ƙara da cewa matafiyan na kan hanyar komawa garinsu na asali ne “domin yin bukukuwan sallah tare da iyalansu.”

Amnesty ta yi kira da a gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da tabbatar anhukunta masu hannu a cikinsa.

Kwankwaso ya fusata

Jagoran jam’iyyar adawa ta NNPP kuma tsohon Gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi tir da kisan, inda ya nemi a gudanar da bincike.

Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso ya bayyana harin a matsayin “rashin adalci”

Ya jaddada cewa duk wani ɗan Nijeriya na da ‘yancin yin tafiya a ƙasar nan ba tare da fargabar cin zarafi ko tsangwama ba.

“Abin da kowa ya sani shi ne, ya zama wajibi a bar ‘yan kasa su yi tafiya a duk faɗin kasar nan ba tare da fuskantar wata barazana ko cin zarafi ba.

“Ina kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike a kan wannan lamari mai tayar da hankali tare da tabbatar da an hukunta masu hannu a ciki,” in ji Kwankwaso.

Atiku ya bayyana kaɗuwarsa

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar ya bayyana kaɗuwarsa tare kiran mahukunta da su gaggauta ɗaukar matakan da suka dace kan lamarin

A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya ce “ina matuƙar baƙin ciki da rahotannin kisan gillar da aka yi wa wasu mafarauta a Jihar Edo.

“Ina miƙa ta’aziyyata ga iyalai da ’yan uwan waɗanda abin ya shafa.

“Wannan mummunan lamari yana buƙatar cikakken bincike domin ganowa da kuma tabbatar da cewa an gurfanar da waɗanda ke da hannu a ciki.”

Atiku ya kara da cewa “kare rayukan waɗanda da ba su ji ba ba su gani ba dole ne ya kasance abu mai muhimmanci.

“Kuma ina kira ga hukumomi da su gaggauta ɗaukar mataki don hana sake afkuwar wannan lamari na ɗaukar doka a hannu.”

A tabbatar an kamo masu hannu a aika-aikar — Tinubu

Shi ma Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.

“Ba za a bari miyagu su ci gaba da zubar da jinin ‘yan Nijeriya ba tare da hukunta su ba.

“Dole ne a yi adalci,” a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan sa Kai Arewa Jihar Edo mafarauta Rabi u Musa Kwankwaso

এছাড়াও পড়ুন:

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

 

Da yake mayar da martani ga wannan zargin na Amurka, Bwala ya ce gwamnatin Tinubu tana jajircewa wajen kare dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da addini ba, yana mai cewa Amurka da Nijeriya sun dade suna hadin gwiwa a yaki da ta’addanci.

 

“Shugaba Bola Tinubu da Shugaba Donald Trump suna da kudiri iri ɗaya a yaƙi da ta’addanci da duk wani nau’in ta’addanci a kan bil’adama,” in ji Bwala.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025 Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?