Aminiya:
2025-06-14@23:58:17 GMT

Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya

Published: 28th, March 2025 GMT

Kisan wasu matafiya ’yan Arewa da aka yi a garin Uromi da ke Ƙaramar Hukumar Arewa maso Gabashin Esan ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya.

A bayan nan ne wasu hotunan bidiyo da aka yaɗa a shafukan sada zumunta suka nuna wasu mutane ɗauke da makamai suna far wa matafiyan da suka taso daga Kudanci zuwa Arewacin Nijeriya.

Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand

Hotunan bidiyon sun nuna yadda aka yi wa waɗanda abin ya shafa jina-jina sannan aka cinna musu wuta suka ƙone ƙurmus.

Tuni dai gwamnatin Edo ta yi Allah wadai da lamarin wanda ya faru a ranar Alhamis tare da ba da umarnin ƙaddamar da bincike a kai.

Wata sanarwa da Sakataren Labarai na Fadar Gwamnatin Edo, Fred Itua ya fitar, ta tabbatar da cewa ’yan sa- kai ne suka kai harin

Sanarwar ta ambato Gwamna Monday Okpebholoce na shan alwashin hukunta “masu laifin.”

“Binciken farko-farko ya nuna cewa matafiya ne da suka taso daga Fatakwal na Jihar Ribas suka ratso ta garin, sai ’yan banga suka kama su da tunanin cewa ɓatagri ne,” kamar yadda Fred Itua ya bayyana.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana adadin mutanen da aka kashe ba a harin, amma ta ce Gwamna Okpebholo ya ziyarci garin a ranar Juma’a, inda ya yi alƙawarin gano waɗanda suke da hannu domin su fuskanci hukunci.

Yayin ziyarar da ya kai wurin da lamarin ya faru, Gwamna Okpebholo ya yaba wa shugabannin ’yan arewacin Nijeriya “bisa yadda suka kwantar da al’amarin cikin hikima” in ji sanarwar.

Mutum 16 aka kashe ’yan asalin Jihar Kano — Amnesty

Ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta ce mutane 16 aka kashe kuma ’yan asalin Jihar Kano ne.

“’Yan sa-kai sun tare matafiyan, suka fito da su daga motarsu, suka yi musu duka, sannan suka cinna musu wuta,” a cewar wani saƙo da Amnesty ta wallafa a shafukan sada zumunta.

Ta ƙara da cewa matafiyan na kan hanyar komawa garinsu na asali ne “domin yin bukukuwan sallah tare da iyalansu.”

Amnesty ta yi kira da a gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da tabbatar anhukunta masu hannu a cikinsa.

Kwankwaso ya fusata

Jagoran jam’iyyar adawa ta NNPP kuma tsohon Gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi tir da kisan, inda ya nemi a gudanar da bincike.

Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso ya bayyana harin a matsayin “rashin adalci”

Ya jaddada cewa duk wani ɗan Nijeriya na da ‘yancin yin tafiya a ƙasar nan ba tare da fargabar cin zarafi ko tsangwama ba.

“Abin da kowa ya sani shi ne, ya zama wajibi a bar ‘yan kasa su yi tafiya a duk faɗin kasar nan ba tare da fuskantar wata barazana ko cin zarafi ba.

“Ina kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike a kan wannan lamari mai tayar da hankali tare da tabbatar da an hukunta masu hannu a ciki,” in ji Kwankwaso.

Atiku ya bayyana kaɗuwarsa

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar ya bayyana kaɗuwarsa tare kiran mahukunta da su gaggauta ɗaukar matakan da suka dace kan lamarin

A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya ce “ina matuƙar baƙin ciki da rahotannin kisan gillar da aka yi wa wasu mafarauta a Jihar Edo.

“Ina miƙa ta’aziyyata ga iyalai da ’yan uwan waɗanda abin ya shafa.

“Wannan mummunan lamari yana buƙatar cikakken bincike domin ganowa da kuma tabbatar da cewa an gurfanar da waɗanda ke da hannu a ciki.”

Atiku ya kara da cewa “kare rayukan waɗanda da ba su ji ba ba su gani ba dole ne ya kasance abu mai muhimmanci.

“Kuma ina kira ga hukumomi da su gaggauta ɗaukar mataki don hana sake afkuwar wannan lamari na ɗaukar doka a hannu.”

A tabbatar an kamo masu hannu a aika-aikar — Tinubu

Shi ma Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.

“Ba za a bari miyagu su ci gaba da zubar da jinin ‘yan Nijeriya ba tare da hukunta su ba.

“Dole ne a yi adalci,” a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan sa Kai Arewa Jihar Edo mafarauta Rabi u Musa Kwankwaso

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Ba tare da saninmu ba, yawancin al’ummar Afirka musamman ma naYammacin Afirka suna fama da abinda ake kira da suna irin hali ko yanayin da aka shiga sanadiyar lamarin cinikin Bayi.Bayan shekara 100 da aka yi daga shekarar 1801 zuwa 1901, an yi wani kokarin da ake yi ma kallon tamkar wani takune na yadda za’a kubuta daga irin cin fuskar da ake yi kowace rana.

Kafin dai a tsunduma sosai cikin lamarin cinikin Bayi, yana da matukar kyau a fara yin bayani kan yadda abin ya fara:Lamarin cinikin Bayi ba manufa bace ta Yammacin Turai.Duk lamarin ya zarce wani hasashen da za’a iya yi ko wani rubutun,da aka yi aka aje.Idan kuma aka duba ta bangaren nahiyar Afirka ita kanta, sha’anin cinikin Bayi ya kasance nae kafin zuwa Turawa shekaru darurra da suka gabata,lamarin kuma yana ci gaba har zuwa halin da ake ciki yanzu ,ana iya tunawa da yadda Bayin da aka saya a nahiyar Afirka ake tafiya da su ta hanyar Sahara wadda take da Yashi,ta haka ne aka fara musanyar mutane,a bada su ,sannan a amshi wasu abubuwa”.

Afirka, a matsayinta na nahiya ita ma ta dandana kudarta idan ana maganatr cinikin Bayi har zuwa shenture 14 wanda ya zarce shekara 1000 ke nan:10 ga duniyar Larabawa,sai kuma 4 ga sauran yammacin Turai. Ciniki Bayi na bangaren Larabawa ya far ne a karni na 8 hakan ta kasance ne saboda yadda addinin musulunci ya hana Musulmai daga bautar da ‘yan’uwansu. Duk da an hana hakan bukatar mutane su rika yin wasu ayyuka,don haka shi yasa Larabawa suke zuwa nahiyar Afirka domin su samu Bayin.Da farko sun tsaya ta gabas ta gabar ruwa na, Rift Balley, amma yayin da suke kasuwanci, sai suka rika yada addininsu na musulunci. Wannan ya nuan ke nan wurin da yake ana ta lamarin fataucin Bayi,ya zama yanzu babu yadda za su yi su samu Bayi daga can,don haka sannu a hankali sai suka maida akalarsu zuwa yammacin Afirka.domin idon su ya fara budewa saboda ai addinin musulunci ya hana cinikin Bayi. Wannan shi yake nuna duk yadda Larabawa suke bukatar samun ‘yan Afirka a matsayin Bayi ya zo karshe.

Abu daya wanda yake kamar sun yi kama da juna tsakaanin Larabawa da Yammacin Turai shi ne suna yin amfani ne da addini, Musulunci da Kiristanci domin su samu bakin bada dalilin da yasa suke kasuwancin mutane.A kokarin da muke na nuna yin kama da juna, sai mun yi bayani dangane da bambancin, tsakanin kasuwancin na hanyar da ake bi ta Yashi, da kuma ta wani babban Kogi da kuma na ake bi ta babban ruwa ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita