Aminiya:
2025-04-30@19:46:51 GMT

Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand

Published: 28th, March 2025 GMT

Kimanin mutum 150 ne suka riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wata mummunar girgizar ƙasa daban-daban da suka auku a ƙasashen Myanmar da Thailand.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito cewa girgizar ƙasar wadda ta auku a wannan Juma’ar ta jikkata ɗaruruwan mutane a yayin da baraguzai suka danne gommai.

An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara ’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano

Hukumar binciken yanayin ƙasa ta Amurka (USGS) ta bayyana cewa an fuskanci wata mummunar girgizar kasa har kashi biyu masu ƙarfin awo 7.7 da 6.4 a Myanmar, tare kuma da wata girgizar ƙasar mai karfi da ta yi ɓarna a kasar Thailand wacce ta shafi wasu wurare a yankin.

Girgizar ƙasa ta farko ta afku ne a wani wuri mai nisan kilomita 16 a arewa maso yammacin birnin Sagaing wacce ta mamayi aƙalla kilomita 10 da misalin ƙarfe 12:50 na daren ƙasar ranar Juma’a, a cewar hukumar binciken yanayin ƙasar ta Amurka USGS.

Gwamnatin ƙasar da za ta gudanar da bincike kan lamarin cikin gaggawa tare da fara ayyukan ceto da kuma samar da kayayyakin agajin jin kai, kamar yadda ta bayyana a shafinta na Telegram.

A cewar wasu shaidu biyu daga garin Taungnoo da ke yankin Bago da suka zanta da kamfanin dillancin labaru na Reuters, aƙalla mutane uku ne suka mutu bayan wani ɓangare na wani masallaci ya rufta.

Girgizar ƙasar ta yi kaca kaca da cibiyar kasuwancin Bangkok haɗi da tituna da gadoji da kuma wani dogon gini mai hawa 30 da ko kammala shi ba a yi ba.

Tuni dai Firaministan Thailand, Paetongtarn Shinawatra ya ayyana dokar ta ɓaci a Bangkok.

Haka kuma, sojojin da ke mulki a Myanmar sun sanar da ayyana dokar ta ɓaci a babban birnin da kuma birni na biyu mafi girma a ƙasar da wasu jihohi shida.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Girgizar ƙasa Myanmar girgizar ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai

A yammacin ranar Talata Arsenal ta karbi bakuncin PSG a matakin wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Turai na bana.

An dai barje gumi ne a filin wasa na Emirates, inda PSG ta yi wa Arsenal ci daya mai ban haushi har gida.

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno

PSG ta fara cin ƙwallo ta hannun Ousmane Dembele a minti na huɗu da take leda, haka suka je hutu har da zagaye na biyu, amma Gunners ba ta farke ba.

Wannan shi ne karo na biyu da suka fuskanci juna a Champions League a kakar nan, inda Gunners ta yi nasarar cin 2-0 a Emirates a cikin watan Oktoba.

Arsenal da Paris Saint-Germain da Inter Milan da Barcelona su ne kungiyoyin da 4 da suka kai matakin zagayen daf da karshe na gasar.

A wannan Larabar ce kuma za a yi karon batta tsakanin Inter Milan da Barcelona, bayan kimanin shekara 15 da aka yi makamancin wannan karawar daf da karshe tsakanin ƙungiyoyin biyu a Gasar Zakarun Turai.

Inter Milan ce ta kai zagayen ƙarshe a 2010, sai dai wannan karon Barcelona na fatan lashe kofin bana da zarar ta fuskanci Arsenal ko Paris St Germain a watan gobe.

Sai dai, Barca da Inter sun fuskanci juna a gasar ta zakarun Turai a 2022/23, inda ta Italiya ta yi nasara 1-0 cikin Oktoban 2022 a wasa na biyu suka tashi 3-3 a Sifaniya.

Wannan shi ne karon farko da Barcelona ke fatan kai wa karawar ƙarshe a Champions League, tun bayan da ta lashe na biyar jimilla a 2015.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa