Aminiya:
2025-07-23@04:55:11 GMT

Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4

Published: 26th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta ɗauki mataki na gaba wajen ƙirƙirar sabbin jihohi huɗu a Najeriya.

’Yan majalisa sun tattauna tare da amincewa da karatu na biyu na ƙudirorin da ke neman kafa jihohin Oke-Ogun, Ijebu, Ife-Ijesa, Tiga, Orlu, da Etiti.

Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu

Waɗannan ƙudirori na daga cikin yunƙurin sauya kundin tsarin mulkin 1999.

Shugaban masu rinjaye na majalisa, Hon. Julius Ihonvbere, wanda ya gabatar da ƙudirorin, ya jaddada muhimmancinsu.

“Waɗannan ƙudirori suna nuna buƙatun yankuna daban-daban na ƙasa domin samar da ingantaccen shugabanci da rarraba albarkatu cikin adalci,” in ji shi.

Mataimakin Kakakin Majalisa, Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman, ya jagoranci kaɗa ƙuri’ar murya inda ƙudirorin suka samu amincewa.

An tura su zuwa kwamitin majalisa kan sauya kundin tsarin mulki domin ci gaba da nazari.

Ɗaya daga cikin masu ɗaukar nauyin ƙudirin, Hon. Ghali Mustapha Tijani, ya ce, “Kafa Jihar Tiga zai kusanto da gwamnati ga jama’a tare da haɓaka ci gaba.”

Ana buƙatar amincewar majalisun dokokin jihohi da na ƙasa kafin ƙirƙirar sabbin jihohin a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: karatu Majalisar Wakilai Tsallakewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

Masu ƙarar sun bayyana cewa an ce an bai wa kamfanin kuɗin ne domin samo kuɗin hannu don biyan ma’aikatan wucin gadi da aka ɗauka a zaɓukan ƙananan hukumomi na 2024. Daga bisani kuma, an ce an dawo da kuɗin a matsayin tsaba zuwa hukumar.

Lauyan ICPC, Barr. Enosa Omoghibo, ya shaida wa kotu cewa an shirya fara gurfanar da waɗanda ake zargi ne, amma “ba su halarci kotu ba.”

Sai dai Lauyan waɗanda ake ƙarar, M.A. Magaji (SAN), ya ce abokan hulɗarsa ba su samu takardun shigar da ƙara kotu ba. Ya ƙara da cewa isar da takardu abu ne mai muhimmanci kafin kotu ta iya ci gaba da shari’a.

Daga nan ne kotu ta dage ci gaba da shari’ar zuwa 24 ga Nuwamba, 2025.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
  • HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
  • Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano