Aminiya:
2025-05-29@06:52:25 GMT

Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4

Published: 26th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta ɗauki mataki na gaba wajen ƙirƙirar sabbin jihohi huɗu a Najeriya.

’Yan majalisa sun tattauna tare da amincewa da karatu na biyu na ƙudirorin da ke neman kafa jihohin Oke-Ogun, Ijebu, Ife-Ijesa, Tiga, Orlu, da Etiti.

Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu

Waɗannan ƙudirori na daga cikin yunƙurin sauya kundin tsarin mulkin 1999.

Shugaban masu rinjaye na majalisa, Hon. Julius Ihonvbere, wanda ya gabatar da ƙudirorin, ya jaddada muhimmancinsu.

“Waɗannan ƙudirori suna nuna buƙatun yankuna daban-daban na ƙasa domin samar da ingantaccen shugabanci da rarraba albarkatu cikin adalci,” in ji shi.

Mataimakin Kakakin Majalisa, Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman, ya jagoranci kaɗa ƙuri’ar murya inda ƙudirorin suka samu amincewa.

An tura su zuwa kwamitin majalisa kan sauya kundin tsarin mulki domin ci gaba da nazari.

Ɗaya daga cikin masu ɗaukar nauyin ƙudirin, Hon. Ghali Mustapha Tijani, ya ce, “Kafa Jihar Tiga zai kusanto da gwamnati ga jama’a tare da haɓaka ci gaba.”

Ana buƙatar amincewar majalisun dokokin jihohi da na ƙasa kafin ƙirƙirar sabbin jihohin a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: karatu Majalisar Wakilai Tsallakewa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Amince Da Sauya Kabo Polytechnic Zuwa Jami’ar Kimiyya Da Fasaha Kabo

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’a
  •  Arakci: Idan Birtaniya Ta Ci Gaba Da Batun Dakatar Da Tace Uranium A Iran, Za A Dakatar Da Tattaunawa Da Ita
  • DAGA LARABA: “Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”
  • Tinubu na neman ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje
  • ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano
  • Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn
  • Shugaba Tinubu Ya Amince Da Sauya Kabo Polytechnic Zuwa Jami’ar Kimiyya Da Fasaha Kabo
  • Gwamnatin Kano Zata Gina Masallacin Da Aka Ƙona Masallata A Gezawa
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Wa Yankunan Gaza Hare-hare
  • FCTA Ta Rufe Hedikwatar PDP Ta Ƙasa Saboda Ƙin Biyan Harajin Ƙasa