Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
Published: 21st, March 2025 GMT
Cibiyar ta “ Global 196” ta bakin babban shugabanta ta sanar da cewa a cikin watanni 18 da su ka gabata, ta tattara bayanai akan laifukan yakin da Isra’ila ta tafka a Gaza.” Haka nan kuma cibiyar mai matsuguni a Birtaniya ta ce, ya zuwa yanzu ta tattara da dalilai da su ka dace da ka’idojin shari’a a kotunan manyan laifuka na kasar.
Har ila yau cibiyar ta ce, bayan kammala tattara bayanai a zango na farko, za kuma ta bude shafi na gaba domin kara samun wasu bayanan da za su tabbatar da cewa an yi wa Isra’ilawan hukunci a cikin kasashen duniya, musamman masu dauke da zama ‘yan kasashe biyu.
Wani shiri da wannan cibiyar take da shi,shi ne na samar da wasu cibiyoyin a cikin nahiyoyin duniya da samar da ka’idoji ta fuskar shari’a da su ka dace da na duniya da kuma na kasashe domin farautar wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza, da fitar da sammacin kamo su, saboda su fuskanci shari’a.
Wadanda wannan cibiyar take son ganin sun fuskanci shiri’a, sun hada jami’an sojan HKI, da ‘yan siyasa da duk masu hannu a aikata laifukan yaki.
Ita wannan cibiyar ta kunshi kawance na lauyoyi daga kasashen Malysia, Turkiya, Norway, Canada, Bosnia, da kuma Birtaniya.
Ana kuma sa ran cewa anan gaba wasu lauyoyin daga wasu kasashen duniya za su shiga ciki,musamman a wannan lokacin da HKI ta bude wani sabon kisan kiyashin akan al’ummar Falasdinu.
Cibiyar ta kasa da kasa mai son ganin an yi wa Falasdinawa adalci, ta kuma hada da fitaccen lauyan nan dan kasar Afirka Ta Kudu John Dugard, da kokarin jawo lauyoyi daga dukkakin kasashen duniya.
Cibiyar za ta yi aiki domin ganin a kowace jaha da gunduma ta kasashen duniya an samar da hanyar hukunta wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
A wani taro wanda ya hada ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI da kuma mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara, bangarorin biyu sun tabbatar da cewa an kammala aikin shimfida layin dogo tsakanin garin Shalamcheh na kasar Iran da kuma birnin Basra a kasar Iraki.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jami’an gwamnatocin kasashen biyu na fadar haka, sun kuma jaddada muhimmancin layin dogon da kuma samar da kasuwar babu kudaden fito a kan iyakokin kasashen biyu.
Labarin ya kara da cewa harkokin kasuwanci tsakanin kasashen biyu ya zuwa yanzu ya kai dalar Amurka biliyon $11a ko wace shekara kuma anan saran nan gaba zai iyakaruwa zuwa dalar Amurka biliyon $25.
Rahmatollah Akrami, ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI, da kuma Hazem Majid Naji Al-Khalidi mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara sun jaddada muhimmancin kammala layin dogo tsakanin kasashen biyu, da kuma kasuwar ba kudaden fito tsakanin kasashen biyu. Da kuma fatan zasu yi kokarin amfanar juna gwagwadon abinda zasu iya.