Kwamishinan ‘Yansandan ya yaba wa jami’an da suka gudanar da wannan aiki, inda ya tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a jihar Kano. Dukkanin waɗanda ake zargi suna cikin bincike a sashen binciken laifuka na CID, kuma za gurfanar da su gaban shari’a bayan kammala bincike.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran

A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”

Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan  mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.

A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Asalin Tudun Loess
  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi