Aminiya:
2025-11-02@03:53:24 GMT

Ɗan majalisa ya biya wa ɗaliban mazaɓarsa N45m na jarabawar WAEC

Published: 4th, March 2025 GMT

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Nasarawa da Toto daga Jihar Nasarawa, Honorabul Abdulmumin Ari ya ba da cekin Naira miliyan 45 don biyan kuɗin jarabawar WAEC ga daliban sakandare a mazaɓarsa.

Da yake jawabi a wajen taron a garin Keffi, Abdulmumin Ari ya bayyana cewa kimanin shekara biyar ke nan yake aikin agaza wa daliban mazaɓar a duka matakai don cika alkawura da ya yi a baya.

Ya ce ya yanke shawarar yin haka ne don tallafa wa iyayen ɗalibai marasa galihu don ba su damar cimma burinsu na samar wa ’ya’yansu ilimin zamani dana addini.

Ya ce kawo yanzu ya kashe sama da Naira miliyan 500 a cikin shekara biyar da duka gabata a kan irin wannan aiki.

Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da agazawa a fannin ilimi inda ya bukaci daliban da suka amfana da su tabbatar sun yi amfani da damar yadda ya dace, kana su mayar da hankalinsu ga karatunsu da sauran harkokin rayuwarsu na yau da kullum.

A jawabinsa Shugaban Kwamitin Jarabawar ta WAEC, Malam Awaje Nasarawa da Shugaban Ƙaramar Hukumar ta Keffi, Honorabul Damagani da sauran manyan baki, sun yaba wa dan majalisar, sannan suka bukaci daliban da su yi kyakkyawar amfani da damar don kyautata rayuwarsu a nan gaba.

Wasu daga cikin daliban da suka amfana sun yaba wa dan majalisar inda suka yi addu’ar Allah Ya saka masa da alheri.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Majalisa jarabawar WAEC

এছাড়াও পড়ুন:

Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Wata kotu da ke birnin Madrid ta yi watsi da ƙarar da Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Turai UEFA, LaLiga da Hukumar Kwallon Kafa ta Sipaniya suka shigar kan ƙin amincewa da gasar Super League.

Wannan yana nufin yanzu Real Madrid da sauran ƙungiyyoyin za su iya neman diyyar kudi Euro Milyan 4.

Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 

Real Madrid ta ce, wannan hukuncin ya tabbatar da cewa UEFA ta karya dokokin gasa, kuma ƙungiyyoyi sun rasa maƙuden kuɗaɗe tun daga lokacin da aka dakatar da gasar.

Gasar wacce aka shirya farawa a shekarar 2021 tare da manyan ƙungiyoyin Turai, an yi hasashen zata samar da kusan Yuro miliyan 200 ga ƙungiyoyin da suka shiga.

A nata martanin hukumar UEFA ta dage cewa wannan sabon hukuncin ba ya nufin an dawo ko an amince da a buga gasar Super League ba ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata
  • Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35
  • Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa