Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa
Published: 1st, March 2025 GMT
Farashin kayayyakin abinci kamar masara da shinkafa da gero da dawa da wake da gari da waken soya da dai sauransu sun ragu, musamman a manyan jihohin da ake nomawa, kamar yadda wani bincike da Aminiya ta gudanar ya nuna.
Wannan na faruwa ne gabanin watan Ramadan, wanda aka fara yau Asabar.
Yadda ake ‘Spring rolls’ Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a BornoHaka kuma an ce, jihohin da ba sa noma suna jin tasirin rage farashin kayan abinci.
Masana sun danganta faduwar farashin da aka samu a kasuwa ga karancin kudi da kuma yadda aka yi bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara, wanda hakan ya haifar da faduwa farashin sosai.
Wasu kuma sun ce, yawan shigo da kayan amfanin gona da aka yi a baya-bayan nan shi ma ya taimaka wajen faɗuwar farashin.
Misali, buhun fulawa mai nauyin kilo 50, wanda ake sayar da shi kan Naira 80,000 a ’yan makonnin da suka gabata, yanzu ana sayar da shi ne tsakanin Naira 61,000 zuwa Naira 63,000 ya danganta da kasuwa.
Farashin hatsi ya ragu, sai dai na gyada da koko da dawa da dankalin Turawa da dabino da mai da kayan lambu sun dan yi tsada a kasuwanni da dama da wakilanmu suka zagaya.
KadunaA kasuwar hatsi ta Saminaka da ke Jihar Kaduna, buhun masara mai nauyin kilo 100 da ake sayar da shi tsakanin Naira 70, 000 zuwa Naiera 75,000 a mafi yawan kasuwanni a lokacin girbi, yanzu ya dawo Naira 47,000, yayin da waken soya da ake sayar da shi a baya a kan Naira 110,000, yanzu ya koma Naira 68,000.
Hakazalika, nau’in farin wake da ake sayar da shi kan Naira 150,000 a lokacin girbi, yanzu ya zama N100,000.
A kasuwar Giwa da ke Jihar Kaduna, ana sayar da gero da dawa tsakanin Naira 50, 000 zuwa Naira 51,000 sabanin Naira 79,000 zuwa N80,000 da aka sayar a bara.
Farashin wake ya fadi daga Naira 120,000 zuwa Naira 80,000; farin wake daga N160,000 zuwa Naira 88,000; irin shinkafa, Naira 75,000 zuwa tsakanin N55,000 zuwa N60,000.
TarabaA kasuwar hatsi ta Mutum Biyu da ke Jihar Taraba, farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 100 a yanzu ya kai Naira 45,000 sabanin Naira 50,000 a watan da ya gabata; buhun masara mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi a baya a kan Naira 57,000, yanzu yana tsakanin Naira 40,000 zuwa N45,000; buhun rogo mai nauyin kilo 100, a baya Naira 25,000, yanzu ya zama Naira 18,000 da N19,000.
BinuwaiA Kasuwar Wadata da ke Makurdi a Jihar Binuwai, buhun shinkafa ta gida mai nauyin kilo 50 a yanzu ya kai Naira 26,000 zuwa Naira 29,000 sabanin Naira 45,000 zuwa Naira 55,000 da ake sayar da shi kimanin wata shida da suka wuce.
A Kasuwar Zamani, farashin laka na shinkafa ya ragu daga Naira 2,700 zuwa N1,800, kamar yadda Aminiya ta tattaro.
Haka kuma babban kwandon tumatur, wanda a baya ana sayar da shi kan Naira 45,000, yanzu haka yana kan Naira 30,000 zuwa Naira 35,000.
Farashin mudu na masara da gero da masarar Guinea ya fadi daga Naira 3,200 zuwa Naira 1,200; kwanon dabino, yanzu ya zama N1,800 daga Naira 2,500; robar garri Naira 2,300 daga Naira 3,500; doya 10 tsakanin Naira 10,000 zuwa Naira 15,000 daga tsakanin Naira 12,000 zuwa Naira 18,000.
KanoA Jihar Kano ma wakilinmu ya ruwaito faduwar farashin kayan abinci. A kasuwar Danhassan, farashin kwano na wake ya ragu zuwa Naira 2,500 daga Naira 3,500; gero Naira 1,200 daga Naira 2,700.
A Kasuwar Dawanau, kwanon masara yanzu yana tsakanin Naira 1,200 zuwa Naira 1,300; gero, Naira 1,000 da Naira 1,100; wake tsakanin Naira 2,000 zuwa Naira 2,200 kowane mudu.
NejaA kasuwar Manigi da ke Karamar Hukumar Mashegu a Jihar Neja, farashin buhun jan wake ya fadi daga Naira 200,000 zuwa Naira 90,000 daga Naira 200,000; sai farin wake ya koma Naira 90,000 daga N160, 000; inda farashin farar masara da ja ya koma Naira 40,000 a kowane buhu, maimakon Naira 85,000 da ake sayarwa a baya; gero a yanzu Naira 45,000 ne; dawa Naira 40,000; buhun wake Naira 78,000 sabanin Naira 135,000 a bara.
A Kasuwar Lemu, a halin yanzu ana sayar da buhun gero da masara da dawa kan Naira 42,000; da buhun shinkafa (nika) 100 kilo Naira 108,000.
A garin Bida, wani dan kasuwa, Mohammed Mahmud ya bayyana cewa, farashin shinkafa ’yar gida ya fadi daga Naira 130,000 zuwa Naira 120,000 kan kowane buhu.
Buhun dawa da gero yanzu ya zama Naira 45,000; masara Naira 48,000. A kasuwar karshen mako ta Gwadabe, wakilinmu ya ruwaito cewa, farashin shinkafa da masara da dawa ma sun fadi.
GombeA babbar kasuwar Gombe bangaren ’yan shinkafa da a kwanakin baya ake sayar da babban buhun shinkafar dafawa mai nauyin kilo 100 a kan farashi mabambanta bisa ga kyawun shinkafar da ya kai hawa uku na Naira dubu 180,000 da dubu dari 160,000 da dubu 150,000 yanzu haka farashin ya fadi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kayan abinci Ramadan da ake sayar da shi ya fadi daga Naira 000 sabanin Naira 000 zuwa Naira tsakanin Naira yanzu ya zama zuwa Naira 1 ana sayar da Naira 45 000 daga Naira 2 a kan Naira
এছাড়াও পড়ুন:
Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
Biyo bayan sauya sheka da aka yi kwanan nan, a zauren majalisar dattawa, APC na da kujeru 68; PDP na da 30; LP na da 5; SDP na da 2; NNPP na da 1; APGA na da 1 da kuma kujeru guda biyu da babu kowa, guda daya daga Jihar Edo da daya daga Jihar Anambra.
Masana harkokin siyasa na ganin cewa bisa yadda lamura suke a halin yanzu, adadin na iya haurawa lokacin da majalisar tarayya ta dawo daga hutu, bayan sauya shekar Gwamna Umo Eno na Jihar Akwa Ibom daga PDP zuwa APC. Ana sa ran wasu daga cikin ‘yan majalisar tarayya na jihar za su iya bin sahunsa. A halin yanzu, Jihar Akwa Ibom tana da sanatan PDP guda biyu da ‘yan majalisar wakilai guda bakwai daga PDP.
Tun da aka rantsar da majalisar dattawa ta 10 a watan Yuni 2023, ‘yan majalisa da dama sun koma APC, wanda ya sa jam’yyar na ci gaba da samun gagarumar rinjaye.
Sanata Ibrahim Abdullahi Danbaba, mai wakiltar Sakkwato ta kudu na jam’iyyar PDP, ya koma APC a watan Maris 2024. Da farko, Sanata Ifeanyi Ubah ya canza sheka daga YPP zuwa APC a watan Oktoba 2023 kafin rasuwarsa.
A watan Fabrairu na 2025, Sanata Ned Munir Nwoko, mai wakiltar Delta ta arewa ya bar PDP ya koma APC, yana mai bayyana cewa rikice-rikicen cikin gida a PDP na Delta ya sa ya sauya sheka.
Haka kuma, Sanata Ezenwa Onyewuchi, mai wakiltar Imo ta gabas, wanda aka zaba a karkashin jam’iyyar LP, ya koma APC a watan Yulin 2024, yana mai cewa batutuwan cikin gida ne suka jawo hakan.
Sanata Kawu Sumaila, mai wakiltar Kano ta kudu, wanda aka zabe a karkashin tutun jam’iyyar NNPP, ya sauya sheka zuwa APC a ranar 7 ga Mayu, 2025.
Bayan haka, sanatoci guda uku daga Kebbi da suka hada da Adamu Aliero, mai wakiltar Kebbi ta tsakiyar da Yahaya Abdullahi, mai wakiltar Kebbi ta arewa, da Garba Maidoki, mai wakiltar Kebbi ta kudu, suka sauya sheka daga PDP zuwa APC bayan taron da Shugaban kasa Bola Tinubu ya kira a fadar shugaban kasa.
Kazalika, tun lokacin da aka kaddamar da majalisar wakilai ta 10 a watan Yuni na shekarar 2023, wannan majalisa ya fuskanci lamarin sauya sheka ga wasu daga cikin ‘yan majalisa, wanda ya faru sakamakon sabani na ciki gida a jam’iyyu, matsin lamba na mazabu da kuma sabbin tsarin siyasa wanda hakan ya amfanar da APC.
Da farko, APC ta rike kujeru 175; PDP na da 118; LP na da 35; NNPP na da 19; APGA na da 5; ADC na da 2; SDP na da 2; YPP na da 1; yayin da kujeru uku babu kowa. Gaba daya dai, ‘yan adawar na rike da kujeru 182 fiye da APC. Amma yau, adadin kujerun ’yan adawar ya ragu zuwa 150.
An fara wannan salo ne a ranar 23 ga Yuli, 2024, lokacin da Hon. Idris Salman, mai wakiltar Kabba-Bunu/Ijumu a Jihar Kogi, ya canza sheka daga ADC zuwa APC, yana mai cewa akwai rikicin shugabanci da kuma matsi daga mazabarsa wanda ya sa ya koma jam’iyyar da ke mulki.
A watan Oktoba na 2024, Hon. Chris Nkwonta, mai wakiltar mazabar Ukwa ta yamma da Abiya ta yamma, ya bar PDP ya koma APC a ranar 2 ga Oktoba. Bayan haka a wannan watan, Hon. Sulaiman Abubakar, mai wakitar Gummi/Bukkuyum a Zamfara, shi ma ya fice daga PDP.
Jam’iyyar LP, wacce ta sami karfi a shekara ta 2023, ta fara fuskantar manyan tangarda a karshen shekarar.
A ranar 5 ga Disamba, 2024, ‘yan majalisar LP hudu cikin har da Hon. Chinedu Okere, mai wakiltar Owerri da kewaye da Hon. Mathew Donatus, mai wakiltar Kaura a Kaduna da Hon. Bassey Akiba, mai wakiltar Kalabar da kewaye /Odukpani a Kuros Ribas da Hon. Esosa Iyawe, mai wakiltar Oredo a Jijar Edo, sun koma APC, suna mai bayar da hujja kan rikice-rikicen cikin gida da suka kawo cikas ga kwazonsu.
Hon. Alfred Ajang, mai wakiltar Jos ta kudi / gabas a Filato, ya biyo bayansu a ranar 12 ga Disamba, yana jaddada dalilai masu kama da juna.
Sauyin ya ci gaba har zuwa 2025. A ranar 11 ga watan Fabrairu, Hon. Amos Magaji, mai wakiltar Zangon Kataf/Jaba a Jihar Kaduna) ya sauya sheka daga PDP zuwa APC, yana mai cewa akwai rigima a cikin jam’iyyarsa ta asali.
Washagarin ranar, Hon. Garba Koko, wai wakiltar Kebbi shi ma ya shiga APC daga PDP.
A ranar 18 ga Maris, Hon. Jallo Hussaini Mohammed, mai wakiltar Igabi a Jihar Kaduna, da Hon. Adamu Tanko, mai wakiltar Gurara/Suleja/Tafa a Neja, sun sauya sheka zuwa APC daga PDP, su yi ikirarin cewa rashin jin dadin shugabancin PDP da kuma bayyana kwarin gwiwa a gwamnatin Tinubu su ne makasudin sauya shekarsu.
A ranar 27 ga Maris, Farfesa Chinwe Clara Nnabuife, mai wakiltar Orumba ta arewa/kudu, a Jihar Anambra) ta fice daga YPP zuwa APGA, tana zargin an tsame ta daga ayyukan jam’iyyar.
A watan Mayu na shekara ta 2025, ya zama lokacin da aka sami manyan sauye-sauye. A ranar 6 ga Mayu, ‘yan majalisar PDP guda shida daga Jihar Delta sun canza sheka zuwa APC bayan gwamnan jihar, Sheriff Oborebwori ya jagoranci wannan sauyin. ‘Yan majalisar dai su ne, Hon. Bictor Nwokolo, mai wakiltar Ika arewa, gabas/Ika ta kudu da Hon. Julius Pondi, mai wakiltar Burutu da Hon. Thomas Ereyitomi, mai wakiltar mazabar Warri da Hon. Nicholas Mutu, mai wakiltar Bomadi/Patani) da Hon. Ukodhiko Jonathan, mai wakiltar mazabar Isoko da Hon. Ezechi Nnamdi, mai wakiltar Ndokwa/Ukwuani).
A ranar 15 ga watan Mayu, ‘yan majalisa biyu daga jam’iyyar NNPP, Kabiru Usman da Abdullahi Sani, sun shiga APC. A wannan ranar, dan majalisan PDP mai wakiltar Oriade/Obokun daga Jihar Osun, Oluwole Oke, shi ma ya koma APC.
A ranar 22 ga Mayu, Hon. Sunday Umeha, mai wakitar Udi/Ezeagu daga Jihar Inugu, wanda aka zaba a karkashin LP, ya koma APC, yana cewa har yanzu matsalolin cikin gida na ci gaba da raba kawunan ‘ya’yan jam’iyyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp