Hukumar NPC Za Ta Gudanar Da Kidayar Jama’a Cikin Aminci- Shugaba Tinubu
Published: 25th, February 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu ya ce Najeriya ta dauki wani muhimmin mataki na gudanar da kidayar jama’a da gidaje da aka jima ba a yi ba, inda ya tabbatar da cewa za a gudanar da aikin cikin inganci ta hanyar amfani da fasahar zamani.
Shugaban ya ba da wannan tabbacin ne a wata ganawa da ya yi da jami’an hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) a fadar gwamnati, shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin kidayar jama’a ga tsare-tsare na kasa, tare da jaddada aniyarsa na tabbatar da tattara bayanai masu inganci.
Shugaba Tinubu ya bayyana shirin kafa kwamitin da zai duba kasafin kidayar jama’a da kuma gano hanyoyin samun kudade.
Ya kuma jaddada bukatar hukumar kula da tantance ‘yan kasa (NIMC) ta taka rawar gani wajen gudanar da wannan aiki, tare da tabbatar da samar da ingantattun na’urorin tantancewa da suka hada da tantance fuska da murya.
Shugaban ya bayyana cewa ingantattun bayanan za su haɓaka shirye-shiryen gwamnati, musamman a fannin aikin gona da walwalar jama’a.
Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya tabbatar da kudurin na Tinubu, inda ya bayyana cewa rashin kudi ne ya janyo tsaikon kidayar jama’a.
Ya kuma bayyana cewa, NPC ta riga ta kammala muhimman ayyukan shirye-shirye da suka hada da kidayar jama’a, sannan kuma hukumomin tantancewa da kididdiga daban-daban kamar su NPC, NIMC, NBS, da Ma’aikatar Tattalin Arziki, suna aiki tare don inganta bayanan da ake da su.
Daga Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kidayar Jama a kidayar jama a tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi watsi da zargin cewa gwamnatinsa na ƙoƙarin mayar da Nijeriya kan tsarin ƙasa da ke kan tafarkin jam’iyya ɗaya a ƙarƙashin mulkinsa.
Shugaban ya kore wannan zargin ne a yayin jawabin da ya yi na zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya a zauren majalisar dokokin ƙasar da ke Abuja, yau Alhamis.
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyyaTinubu ya ce masu tunanin cewa APC na son mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya, to tunanin nasu kuskure ne, kuma suna yin sa cikin ruɗani ne.
Ya ce: “Tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu. Kuma ba zai taɓa zama cikin manufofinmu ba.”
Sai dai shugaban ya ce wannan ba zai hana jam’iyyar APC yin maraba da duk wanda ke son shiga cikinta ba.
“Zai kasance mun yi maguɗin siyasa idan muka hana mutane daga wasu jam’iyyun siyasa shigowa jam’iyyar APC,” in ji Tinubu.
Sai dai Tinubun ya ce suna farin cikin da rikicin ci gida da ke addabar jam’iyyun adawa kuma ba zai shawarar yadda za su warware matsalolinsu ba.
“Ina jin daɗin ganin jam’iyyun adawa a cikin ruɗani, saboda hakan nasara ce bangarenmu.
“Najeriya ba za ta zama ƙasa mai jam’iyya ɗaya ba, batun jam’iyya ɗaya bai ta taso ba, amma siyasar za ta taɓarɓare idan muka rufe ƙofa ga masu son shiga APC,” in ji shi.