Hamas, Da OIC Sun Yi Allawadai Da Dirar Mikiyan Da HKI Take Yi A Tulkaram Na Yankin Yamma Da Kogin Joirdan
Published: 22nd, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas wacce take iko da Gaza, a kasar Falasdinu da aka mamaye, ta yi allawadai da kutsawar da firai ministan HKI da kuma ministan yakin sa Israel Kantz zuwa cikin sansanin yan gudun hijira na Tulkaram a yankin yamma da kogin Jordan.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta kara da cewa sojojin HKI sun kutsa cikin sansanonin yan gudun hijira na Palasdinawa a Tulkaram da kuma Jenin tana rusa gidajen falasdinawa tana kuma kora da kuma kashe wadanda suka samu a cikin gidajen nasu.
A wani labarin kuma kungiyar kasashen musulmi ta OIC ta yi allawadai da rushe-rushen gidajen da gwamnatin HKI take yi a yankin yamma da kogin Jordan. Kungiyar ta yi kira da kasashen duniya su sa baki don dakatar da kashe Falasdinawa da kuma korarsu daga gidjensu da kuma rusa wasu gidajen.
Kungiyar ta kara da cewa kutsawa cikin sansanin yan gudun hijira na Tulkaram ci gaba da zaluncin da takewa Falasdinawa a tsawon shekaru 76 da suka gabata. Har’ila yau ministan harkokin wajen Falasdinawa ya yi tir da Natanyahu da kuma Kanzt kan abinda suke aikatawa a garin Tulkaram. Inda suke son korar faladinawa kimani 40000 da suke rayuwa a sansanin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza
Ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta bada sanarwan cewa falasdinawa 7 ne suka mutu a zirin gaza saboda yunwa a cikin sa’o’i 24 da suka gabata wanda ya sa adadin mutanen fa yunwa ta kashe a Gaza kai kai 154.
Tashar talabijan ta Prersstv a nan Tehran ta nakalto Asbitin Nasir na Gaza na cewa yawa wadanda yunwa ta kashe sanadiyyar kofar ragon da HKI ta yiwa Gaza ya kai 154 sannan 89 daga cikinsu jarirai ne suka fi yawa ya zuwa yau Laraba.
A makon da ya gabata ne hukumar abinci ta duniya wato ‘, the United Nations World Food Program (WFP)” ta bada sanarwan cewa 1/3 na mutanen gaza suna kwana da yunwa saboda rashin abinci sanadayar hana shigo da abinci wanda HKI take yi watanni kimani 4 da suka gabata.
WFP ta kara da cewa kashe 25% na mutanen gaza suna fama da karancin abinci ko fari, a yayinda wasu kimani 100,000 daga cikin mata da yara suna fama da karancin abinci mai gina jiki.
Hukumar ta bayyana cewa akwai bukatar a cika gaza da abinci da gaggawa don kawo karshen wannan musibar da gaggawa. Ta ce abincim kadan ba zai wadatar ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci