Aminiya:
2025-04-30@23:45:09 GMT

An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai

Published: 20th, February 2025 GMT

Hukumomin Jami’ar Tarayya da ke Lokoja a Jihar Kogi, sun rufe jami’ar har zuwa wani lokaci domin daƙile ci gaba da asarar rayuka da dukiya.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun magatakarda kuma sakatariyar majalisar Jami’ar, Dokta Rebecca Aimiohu Okojie, a ranar Alhamis kuma ta bayyanawa manema labarai a Lokoja.

Jihar Gombe na ƙarfafa haƙƙoƙin yara masu nakasa — Ƙungiyar JONAPWD NNPP ta rasa Ɗan Majalisa na farko da ya koma APC

Hukumar Jami’ar ta yi zargin cewa, ɗaliban sun tare babbar ƙofar shiga jami’ar ne tun bayan haɗarin da ya yi sanadin mutuwar ɗaliban jami’ar biyar a ranar Litinin, wanda ya sa shiga harabar jami’ar ke da wuya.

“Rufewar jami’ar ya biyo bayan asarar rayuka da ɗalibai biyar suka yi a wani mummunan haɗarin tirela a Felele, ranar Litinin 17 ga Fabrairu, 2025.

“Tun faruwar lamarin, ɗalibai sun tare ƙofar jami’ar duk da kakkausar murya daga gwamnatin jihar da kuma ƙoƙarin da hukumomin jami’ar suka yi na a kwantar da hankula.

“Saboda haka, bisa shawarar hukumomin tsaro na jihar da kuma daƙile ci gaba da asarar rayuka da dukiya, shugaban jami’ar bayan shawarwarin hukumar ta yanke, shawarar a madadin majalisar jami’ar cewa jami’ar, jami’ar da rassanta za a rufe su har sai baba-ta-gani. Ɗalibai za su bar wuraren karatu kafin ƙarfe 12 na rana ranar Alhamis, 20 ga Fabrairu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas

Wata tsohuwa mai shekara 80 a kasar Turkiyya za ta shafe sama da shekara 4 a gidan yari, saboda ta daki jikarta ’yar shekara 18 da silifa a lokacin da suke takaddama.

Asiye Kaytan na zaune tare da jikarta Vural a unguwar Topraklık da ke Denizli a Kudu maso Yammacin Turkiyya.

Tuntuni dai iyayen yarinyar suka rabu, inda tsohuwar mai shekara 80 take kulawa da ita fiye da kanta.

A ranar 9 ga Agustan bara, bayan Vural ta dawo daga aiki, ta fada wa kakarta cewa, za ta fita waje tare da wasu abokanta.

Tsohuwar ta ji tsoron fitar don kare lafiyarta, ta ce ba za ta yarda ba, har ma ta kulle kofa don tabbatar da cewa Vural ba ta iya fita ba.

Zuwa wani lokaci, sai budurwar ta yi kokarin bude kofar, inda Kaytan ta dauko takalmi silifas, ta dake ta.

Vural ta rama dukan da kakarta ta yi mata a ka da wayarta. Kaytan ta fara zubar da jini, inda yarinyar ta kira motar asibiti.

“Jikata ta so fita da yamma, amma na hana ta, na kulle kofa,”

Kaytan ta shaida wa jaridar Sabah News. “Na buge ta a hannu da silifas, sai ta buge ni da wayarta a ka. Lokacin da na fara zubar da jini, sai ta tsorata ta kira motar daukar marasa lafiya.”

Kaytan da jikarta ba su kai kara a kan junansu ba, amma sun bayyana wa wadanda suka amsa da farko yadda tsohuwar ta samu rauni a ka, inda suka kai rahoto a asibitin Jihar Denizli, wanda daga baya aka mika wa ’yan sandan yankin.

An gayyaci matan biyu domin amsa tambayoyi, kuma duk da bayyana cewa sun sasanta rikicin nasu kuma sun yi sulhu, sai aka buɗe ƙofar ƙarar jama’a, kuma ofishin mai shigar da kara na gwamnati ya shigar da karar kakar mai shekara 80.

A shari’ar tasu, masu gabatar da kara sun yi zargin cewa, silifas da Kaytan ta yi amfani da shi wajen dukan jikarta makami ne, kuma yarinyar ’yar shekara 18 ta yi kokarin kare kanta ne a lokacin da ta bugi kakarta da wayarta.

An kuma tuhumi kakar da tauye ’yancin dan-adam saboda ta kulle Vural a cikin gidanta tare da hana ta fita, zargin da zai iya kai ga hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari.

A ranar 25 ga watan Fabrairu ne kotun hukunta manyan laifuka ta 12 ta kasar ta yanke wa Asiye Kaytan hukuncin daurin shekaru 2 da wata 6 a gidan yari saboda laifin ‘tauye ’yancin dan-adam ta hanyar amfani da karfi ko barazana ko yaudara da kuma ƙarin shekaru 2 da watanni 6 kan amfani da “makami” wajen aikata laifin da ta yi wa jikarta.

Daga ƙarshe an rage hukuncin zuwa shekaru 4 da watanni 2, amma lauyan Kaytan ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin.

Idan kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke mata, za ta je gidan yari.

“Zan shiga kurkuku ina da shekara 80? Ta yaya zan zauna a can? An yi mini tiyata, kuma ina tafiya da kyar, za su saka ni a kurkuku saboda silifas,” tsohuwar ta yi kuka.

‘‘Babu wanda ya isa ya daki yaronsa da silifas saboda ana daukar sa a matsayin makami. Ba ni da masaniyan cewa silifas ya zama makami’’, in ji ta. “

An yi wa kakata hukuncin zaman gidan yari ne saboda ta doke ni da silifas, ta hana ni fita daga gidan. Ban so haka ta kasance ba, ban kai karar ta ba, amma an bude karar jama’a,” in ji Asiye Vural.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut