Gwamna Dauda Lawal ya mika makaman da gwamnatinsa ta bayar ga rundunar soji domin kafa hedkwatar rundunar Operation Safe Corridor na jihohin Arewa maso Yamma, a karamar hukumar Tsafe domin kwance damarar makamai, da lalata su da kuma shigar da barayin da suka tuba su koma cikin al’umma.

 

Gwamnan a wajen bikin mika ragamar sansanin da aka samar, ya jaddada aniyar gwamnatin sa na ci gaba da bin sawun ‘yan bindiga har sai an fatattake su da ruguza su da murkushe su.

 

Dokta Lawal ya ce gwamnatin jihar ta samar da wurin ne a matsayin wani shiri na taimakawa gwamnatin tarayya wajen magance matsalar ta’addanci da ya addabi Zamfara da Arewa maso Yamma sama da shekaru goma.

 

A cewarsa, shirin ya yi koyi ne da shirin ‘Operation Safe Corridor’ a yankin Arewa maso Gabas, wanda ya yi nasarar kawar da tsaffin mayakan na Boko Haram tare da dawo da su cikin al’umma.

 

“Amma ga wadanda suka yi niyyar mika makamansu ba tare da wani sharadi ba suna da ‘yancin yin hakan.

 

Da yake jaddada cewa, kafa hedkwatar tsaro ta Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma zai bada damar kwance damara, da wargazawa, da kuma cudanya da tubabbun ‘yan fashi a cikin al’umma.

 

Ya kuma mika godiyarsa ga babban hafsan hafsan sojin kasa, Janar Christopher Musa bisa ganin jihar Zamfara ta cancanci karbar bakuncin rundunar Operation Safe Corridor na 3 a kasar nan.

 

“Ina kuma so in gode wa shugaban kwamitin aiwatar da ayyukan Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma, Manjo Janar EV Onumajoro, wanda kuma shi ne babban hafsan tsaro na hedikwatar tsaron Najeriya, da tawagarsa saboda ganin Zamfara ta dace da kafa hedkwatar wannan muhimmin sashi.

 

Tun da farko, Manjo Janar Onumajuru, wanda ya wakilci babban hafsan hafsoshin tsaron kasar, ya yabawa Gwamna Lawal bisa goyon bayan da yake baiwa sojoji a yakin da ake da ‘yan bindiga a Zamfara.

 

Bayan karbar ragamar wannan sansanin, za mu ci gaba da hada kai da mai girma Gwamna da al’ummar Zamfara, wadanda su ne masu ruwa da tsaki a wannan aiki, domin tabbatar da hadin kai don kwalliya ta biyan kudin sabulu.

 

AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro Zamfara Arewa maso Yamma

এছাড়াও পড়ুন:

Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Umara Zulum ya sanar da fara fitar da kayayyakin robobi zuwa ƙasashen duniya wanda hakan ke nuna wani gagarumin ci gaba a wani ɓangare na ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arzikin Jihar.

Gwamnan ya jaddada cewa, wannan matakin wani ɓangare ne na babbar ajanda na bunƙasa masana’antu da kuma kawar da dogaro da jihar kan yi na kason da gwamnatin tarayya ke bayarwa duk wata.

Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti

Zulum ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis yayin rangadin duba masana’antar robobi ta Borno da ke cikin yankin masana’antu na Maiduguri.

“Ina farin cikin lura cewa mutanen Jihar Borno ba za su sake sayen kayan robobi daga wasu wurare ba, kun ga an sayar da kayayyakin ga ƙasashen maƙwabta da sauran jihohi a cikin Najeriya.”

“Za mu zuba jari sosai a masana’antunmu, don haka nan gaba kaɗan, gwamnatin Jihar Borno ba za ta sake dogara da asusun tarayya ba don ayyukanta na yau da kullum,” in ji Zulum.

Gwamnan ya bayyana cewa masana’antar ta fara fitar da kayayyakinta ga ƙasashen waje, tare da jigilar kayayyakin filastik da aka gama zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Chadi da Jamhuriyar Kamaru.

Zulum ya lura cewa an fara gina cibiyar ne a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Kashim Shettima, amma an farfaɗo da ita a matsayin wani ɓangare na shirin murmurewa da ci gaban gwamnatinsa.

Wasu daga cikin kayan robobin

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai