Gwamna Dauda Lawal ya mika makaman da gwamnatinsa ta bayar ga rundunar soji domin kafa hedkwatar rundunar Operation Safe Corridor na jihohin Arewa maso Yamma, a karamar hukumar Tsafe domin kwance damarar makamai, da lalata su da kuma shigar da barayin da suka tuba su koma cikin al’umma.

 

Gwamnan a wajen bikin mika ragamar sansanin da aka samar, ya jaddada aniyar gwamnatin sa na ci gaba da bin sawun ‘yan bindiga har sai an fatattake su da ruguza su da murkushe su.

 

Dokta Lawal ya ce gwamnatin jihar ta samar da wurin ne a matsayin wani shiri na taimakawa gwamnatin tarayya wajen magance matsalar ta’addanci da ya addabi Zamfara da Arewa maso Yamma sama da shekaru goma.

 

A cewarsa, shirin ya yi koyi ne da shirin ‘Operation Safe Corridor’ a yankin Arewa maso Gabas, wanda ya yi nasarar kawar da tsaffin mayakan na Boko Haram tare da dawo da su cikin al’umma.

 

“Amma ga wadanda suka yi niyyar mika makamansu ba tare da wani sharadi ba suna da ‘yancin yin hakan.

 

Da yake jaddada cewa, kafa hedkwatar tsaro ta Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma zai bada damar kwance damara, da wargazawa, da kuma cudanya da tubabbun ‘yan fashi a cikin al’umma.

 

Ya kuma mika godiyarsa ga babban hafsan hafsan sojin kasa, Janar Christopher Musa bisa ganin jihar Zamfara ta cancanci karbar bakuncin rundunar Operation Safe Corridor na 3 a kasar nan.

 

“Ina kuma so in gode wa shugaban kwamitin aiwatar da ayyukan Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma, Manjo Janar EV Onumajoro, wanda kuma shi ne babban hafsan tsaro na hedikwatar tsaron Najeriya, da tawagarsa saboda ganin Zamfara ta dace da kafa hedkwatar wannan muhimmin sashi.

 

Tun da farko, Manjo Janar Onumajuru, wanda ya wakilci babban hafsan hafsoshin tsaron kasar, ya yabawa Gwamna Lawal bisa goyon bayan da yake baiwa sojoji a yakin da ake da ‘yan bindiga a Zamfara.

 

Bayan karbar ragamar wannan sansanin, za mu ci gaba da hada kai da mai girma Gwamna da al’ummar Zamfara, wadanda su ne masu ruwa da tsaki a wannan aiki, domin tabbatar da hadin kai don kwalliya ta biyan kudin sabulu.

 

AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro Zamfara Arewa maso Yamma

এছাড়াও পড়ুন:

MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122

Hukumar dake kula da ‘yan hijira dake karkashin MDD ta sanar da cewa, mutanen yake-yake da rikice-su ka tilastawa yin hijira a duniya ya kai miliyan 122.

A yau Alhamis ne dai hukumar dake kula da ‘yan hijirar ta bayyana haka, tana kai kara da cewa; gajiyawar da aka yi na warware fadace-fadace da rikicen da suke faruwa a duniya ne su ka kara yawan ‘yan hijirar, daga ciki har da kasashen Sudan da kuma Ukiraniya.

Haka nan kuma ta ce; Tun daga 2015 ne ake samun koma baya na kudaden da ya kamata a rika bayarwa domin taimakawa ‘yan hijira.

Shugaban hukumar ‘yan hijirar ta MDD Filippo Grandi wanda ya gabatar da rahoto akan halin da ake ciki, ya yi ishara da cewa, tun daga watan Aprilu na wannan shekara ta 2025 da ake ciki an sami karuwar mutane miliyan biyu da su ka zama ‘yan hijira, duk da cewa wani adadin da ya kai mutane miliyan biyu ‘yan kasar Syria sun koma kasarsu bayan faduwar gwamnatin Basshar Asad.

Filippo Grandi ya ce rikice-rikicen kasar Myanmar, da yakin Ukiraniya da Sudan su ne ummul-haba’isin karuwar ‘yan hijirar da kuma gajiyawa wajen kawo karshen hakan.

Kasar Amurka tana cikin wadanda su ka rage yawan taimakon kudaden da suke bayarwa a harkar agaji, yayin da kasashe kamar Birtaniya da wasu kasashen turai suke bayar da kadan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane