Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bibiyar ’yan ta’adda har sai an fatattake su, an ruguza su tare da murƙushe su.

Gwamnan ya miƙa kayan aikin da gwamnatin jihar Zamfara ta samar domin kafa hedikwatar tsaro ta dakarun sojin ‘Operation Safe Corridor’ na jihohin Arewa maso Yamma.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa ‘Operation Safe Corridor’ zai ta tabbatar da canja ƙwaƙwale, haɗe kai magance duk al’amuran da suka shafi ’yan bindiga.

Sanarwar ta ƙara da cewa, an tsara shirin ne a ƙarƙashin Operation Safe Corridor a yankin Arewa maso Gabas, wanda ya yi nasarar sauya ƙwaƙwalen tsoffin mayaƙan Boko Haram tare da gyara tubabbun su.

“Shirin Arewa maso Yamma na neman bayar da tsarin tuba ga mutanen da ke da hannu cikin ayyukan ‘yan bindiga. Wannan yunƙurin zai ƙunshi horar da su wajen sana’o’i, canja musu tunani, da sake musu fasalin aƙida.”

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya ce gwamnatin jihar ta samar da wurin ne a matsayin wani shiri na taimaka wa gwamnatin tarayya wajen magance matsalar ‘yan bindiga da ya addabi Zamfara da Arewa maso Yamma sama da shekaru goma.

“Ina so in sake mayar da alƙawarin da gwamnatinmu ta yi na tallafa wa waɗannan tsare-tsare da sauran dabaru masu inganci da ake amfani da su wajen kai wannan yaƙi zuwa ga ’yan bindigar har sai an fatattake su yadda ya kamata tare da murƙushe su.

“Amma ga waɗanda suka yi niyyar miƙa makamansu ba tare da wani sharaɗi ba da son rai, suna da ‘yancin yin hakan. Kafa Hedikwatar Rundunar Tsaro ta Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma zai ba da dama da masu niyyar tuba tare da gyara musu ɗabi’arsu.

“A kan wannan batu, ina so in miƙa godiyata ga Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Musa, na ganin jihar Zamfara ta cancanci karbar baƙuncin Operation Safe Corridor na 3 a ƙasar nan.

“Ina kuma so in gode wa shugaban kwamitin aiwatar da ayyukan Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma, Manjo Janar EV Onumajoro, wanda kuma shi ne Babban Hafsan Harkokin Tsaro na Hedikwatar Tsaron Nijeriya, da tawagarsa saboda ganin Zamfara ta dace da kafa hedikwatar wannan muhimmin dakaru.

“Daga ƙarshe muna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kuma Babban Kwamandan Askarawan Tarayyar Nijeriya, bisa dukkan ƙoƙarinsa da goyon bayansa ga hukumomin tsaro da ke aiki a jihar.

“Abin da ake buƙata shi ne ƙara ƙarfafa nasarorin da aka samu wajen murƙushe ayyukan ’yan bindiga da sauran aikata laifuka. Ina so in tabbatar muku da ƙudurinmu na yin komai don ganin cewa wannan shirin ya yi nasara. A garemu a yau, wannan shi ne haihuwar sabuwar Zamfara mai tsari.

“Da waɗannan ‘yan kalamai, ina so in miƙa wannan cibiyar domin yin aiki a matsayin hedikwatar Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma domin amfanin jihar Zamfara da kuma ƙyaunatacciyar ƙasarmu Nijeriya.”

Tun da farko, Manjo Janar Onumajuru, wanda ya wakilci Babban Hafsan Tsaron Ƙasar, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa goyon bayan da yake baiwa sojoji a yaƙin da ake da ’yan bindiga a Zamfara.

“Operation Safe Corridor dakaru ce mai aiki da cikakken tsari. Tana aiki a matsayin hanyar samar da zaman lafiya. Bayan karbar ragamar wannan ginin, za mu ci gaba da haɗa kai da Gwamna da al’ummar Zamfara, waɗanda su ne masu ruwa da tsaki a wannan aiki, domin tabbatar da haɗin kai da samun nasara.

Aminu Dalhatu/Gusau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lawal Tsaro Zamfara Arewa maso Yamma jihar Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

A ranar 30 ga wata ne shugabannin kasashen Sin da Amurka suka gana da juna a birnin Busan na kasar Koriya ta Kudu, lamarin da ya jawo hankulan kasa da kasa, inda shugabannin 2 suka yi musayar ra’ayoyi dangane da huldar da ke tsakanin kasashen 2 da al’amuran da suka jawo hankulansu. Sun amince da inganta hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin tattalin arziki da cinikayya da makamashi da kyautata mu’amalar al’adu.

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jaddada cewa, yana son hada kai da shugaba Donald Trump na Amurka wajen aza harsashi mai kyau na raya huldar da ke tsakanin kasashen 2, tare da samar wa juna kyakkyawan yanayin samun ci gaba. A nasa bangaren, shugaba Trump ya ce, kasar Sin, abokiyar Amurka ce mafi girma. Kasashen 2 za su hada kansu wajen samun nasarar gudanar da manyan ayyuka da dama a duniya. Nan gaba Amurka da Sin za su kara samun nasara a hadin gwiwarsu. Shugabannin 2 sun amince su rika yin mu’amala da juna. Shugaba Trump yana sa ran kai ziyara a kasar Sin a farkon shekara mai zuwa, ya kuma gayyaci shugaba Xi ya ziyarci Amurka.

Masharhanta sun yi nuni da cewa, ganawar shugabannin 2 ta sanya tagomashi kan kyautatuwar huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, ta kuma tsara manufar raya huldar kasashen 2 a nan gaba, tare da kwantar da hankulan kasashen duniya.

Abubuwan tarihi da kuma hakikanin abubuwa sun nuna cewa, wajibi ne Sin da Amurka su zama abokan juna. A wannan muhimmin lokaci, ganawar da shugabannin kasashen 2 suka yi ta sake tsara manufar kyautata da raya huldar da ke tsakanin kasashen 2. Muddin kasashen 2 suka aiwatar da muhimman daidaito da shugabannin 2 suka cimma, da mutunta ruhin adalci, tare da martaba juna da samun moriyar juna, to, za a raya huldar da ke tsakanin kasashen 2 ba tare da wata matsala ba, da kuma kara samar da kwanciyar hankali da tabbaci a duniya. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara