Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bibiyar ’yan ta’adda har sai an fatattake su, an ruguza su tare da murƙushe su.

Gwamnan ya miƙa kayan aikin da gwamnatin jihar Zamfara ta samar domin kafa hedikwatar tsaro ta dakarun sojin ‘Operation Safe Corridor’ na jihohin Arewa maso Yamma.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa ‘Operation Safe Corridor’ zai ta tabbatar da canja ƙwaƙwale, haɗe kai magance duk al’amuran da suka shafi ’yan bindiga.

Sanarwar ta ƙara da cewa, an tsara shirin ne a ƙarƙashin Operation Safe Corridor a yankin Arewa maso Gabas, wanda ya yi nasarar sauya ƙwaƙwalen tsoffin mayaƙan Boko Haram tare da gyara tubabbun su.

“Shirin Arewa maso Yamma na neman bayar da tsarin tuba ga mutanen da ke da hannu cikin ayyukan ‘yan bindiga. Wannan yunƙurin zai ƙunshi horar da su wajen sana’o’i, canja musu tunani, da sake musu fasalin aƙida.”

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya ce gwamnatin jihar ta samar da wurin ne a matsayin wani shiri na taimaka wa gwamnatin tarayya wajen magance matsalar ‘yan bindiga da ya addabi Zamfara da Arewa maso Yamma sama da shekaru goma.

“Ina so in sake mayar da alƙawarin da gwamnatinmu ta yi na tallafa wa waɗannan tsare-tsare da sauran dabaru masu inganci da ake amfani da su wajen kai wannan yaƙi zuwa ga ’yan bindigar har sai an fatattake su yadda ya kamata tare da murƙushe su.

“Amma ga waɗanda suka yi niyyar miƙa makamansu ba tare da wani sharaɗi ba da son rai, suna da ‘yancin yin hakan. Kafa Hedikwatar Rundunar Tsaro ta Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma zai ba da dama da masu niyyar tuba tare da gyara musu ɗabi’arsu.

“A kan wannan batu, ina so in miƙa godiyata ga Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Musa, na ganin jihar Zamfara ta cancanci karbar baƙuncin Operation Safe Corridor na 3 a ƙasar nan.

“Ina kuma so in gode wa shugaban kwamitin aiwatar da ayyukan Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma, Manjo Janar EV Onumajoro, wanda kuma shi ne Babban Hafsan Harkokin Tsaro na Hedikwatar Tsaron Nijeriya, da tawagarsa saboda ganin Zamfara ta dace da kafa hedikwatar wannan muhimmin dakaru.

“Daga ƙarshe muna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kuma Babban Kwamandan Askarawan Tarayyar Nijeriya, bisa dukkan ƙoƙarinsa da goyon bayansa ga hukumomin tsaro da ke aiki a jihar.

“Abin da ake buƙata shi ne ƙara ƙarfafa nasarorin da aka samu wajen murƙushe ayyukan ’yan bindiga da sauran aikata laifuka. Ina so in tabbatar muku da ƙudurinmu na yin komai don ganin cewa wannan shirin ya yi nasara. A garemu a yau, wannan shi ne haihuwar sabuwar Zamfara mai tsari.

“Da waɗannan ‘yan kalamai, ina so in miƙa wannan cibiyar domin yin aiki a matsayin hedikwatar Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma domin amfanin jihar Zamfara da kuma ƙyaunatacciyar ƙasarmu Nijeriya.”

Tun da farko, Manjo Janar Onumajuru, wanda ya wakilci Babban Hafsan Tsaron Ƙasar, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa goyon bayan da yake baiwa sojoji a yaƙin da ake da ’yan bindiga a Zamfara.

“Operation Safe Corridor dakaru ce mai aiki da cikakken tsari. Tana aiki a matsayin hanyar samar da zaman lafiya. Bayan karbar ragamar wannan ginin, za mu ci gaba da haɗa kai da Gwamna da al’ummar Zamfara, waɗanda su ne masu ruwa da tsaki a wannan aiki, domin tabbatar da haɗin kai da samun nasara.

Aminu Dalhatu/Gusau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lawal Tsaro Zamfara Arewa maso Yamma jihar Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta saki tare da hada wadanda aka yi garkuwa da su talatin da biyar tare da iyalansu.

 

Sun kunshi mata goma sha shida da yara goma sha tara daga Kagara, Tegina da Agwara, bayan sun shafe makonni a hannun ‘yan sanda da ke tsare da kuma kawar da hankalinsu daga barayin da ke Minna.

 

Kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman ya bayyana haka a lokacin wani takaitaccen bayani da ya mikawa shugaban karamar hukumar gidan rediyon Ayuba Usman Katako a Minna.

 

Kwamishinan ‘yan sandan wanda mataimakin kwamishinan ‘yan sanda Ibrahim Adamu ya wakilta, ya bayyana cewa za’a sake haduwa da wadanda abin ya shafa da iyalansu domin sun kasance karkashin kulawar ‘yan sanda tare da tallafi da kulawar da suka dace daga gwamnatin jihar Neja.

 

A cewarsa, hakan ya fara ne a ranar 3 ga watan Yulin 2025 lokacin da aka samu labari daga wata majiya mai tushe da ke nuna cewa wadanda abin ya shafa na kaura daga Birnin-Gwari a jihar Kaduna zuwa wasu yankuna.

 

Jami’an ‘yan sanda sun yi kaca-kaca da rukunin farko na st Agwara a kokarin da suke na tsallakawa kogin zuwa wasu kauyukan New-Bussa na jihar Neja tare da ceto mata biyar da kananan yara shida.

 

A yayin da ake gudanar da tambayoyi, an bayyana cewa ‘yan bindigar na yin kaura daga Birnin-Gwari zuwa wasu unguwanni kuma rundunar ‘yan sandan da ke aiki a hanyar Mekujeri zuwa Tegina ta cafke kashi na biyu tare da mata hudu da kananan yara bakwai, yayin da kuma aka kama wani rukunin tare da direban da ya tafi da su.

 

Bincike ya nuna cewa direban, Yusuf Abdullahi na Birnin-Gwari ya je sansaninsu ne domin kai mutanen da abin ya shafa, kuma yana kan bincike don tabbatar da hadin gwiwarsa a ayyukansu.

 

Kwamishinan ‘yan sandan, Adamu Abdullahi Elleman, ya tabbatar da cewa tun da aka tsare wadanda abin ya shafa, an ba su wasu shawarwari da nasiha, da abinci da kuma kayan kwanciya.

 

Ya kara da cewa, bayan samun takardar izinin da ya kamata, ana mika wadanda abin ya shafa ga shugaban karamar hukumar da ‘yan uwansu tare da yin kira ga jama’a da su baiwa ‘yan sanda bayanan da suka dace a duk lokacin da aka lura da al’amura domin gaggauta shiga tsakani.

 

PR ALIYU LAWAL.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau