Aminiya:
2025-09-18@08:25:41 GMT

N50,000 aka biya ni don safarar harsasai zuwa Abuja – Matashi

Published: 12th, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Filato, ta kama wani matashi tare da wasu mutum uku kan zargin safarar harsasai daga Jos zuwa Abuja.

Matashin ya bayyana cewa ’yan ta’adda sun biya shi Naira 50,000 domin ya karɓo harsasai daga Jos zuwa Abuja.

Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum

“Ni mazaunin Abuja ne.

Makonni biyu da suka wuce, wani mutum ya aike ni domin karɓo masa harsasai a Jos zuwa Abuja.

“Ya tabbatar min babu wata matsala da zan fuskanta, amma a hanya jami’an tsaro suka kama mu ni da wasu mutum uku,” in ji matashin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, yayin da yake holen waɗanda ake zargi, ya ce an kama su ne bayan samun rahoton sirri kan ayyukansu.

“Mun kama waɗanda ake zargin ne bayan samun sahihan bayanan sirri.

“Rundunar na ci gaba da bincike, kuma da zarar an kammala, za a miƙa su zuwa kotu domin fuskantar hukunci.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Harsasai Masu Safarar Makamai matsalar matsalar tsaro Safara

এছাড়াও পড়ুন:

Fasahar AI ta gano cutar da za ta kama mutane a shekara 10 masu zuwa

Masu bincike a Turai sun yi amfani da fasahar ƙirƙirariyyar basira ta AI don yin hasashen matsalolin lafiya da ɗaiɗaikun mutane za su iya fuskanta cikin shekaru goma masu zuwa ko fiye na rayuwarsu.

Sun ce fasahar na amfanin da bayanan rashin lafiyar da mutum ya yi a baya, domin hasashen cutuka fiye da dubu ɗaya da ke barazanar kama mutum, tun ma kafin soma bayyana.

An wallafa cikakkun bayanan binciken – da suka bayyana da gagarumar nasara – a mujallar kiwon lafiya ta Nature.

An horar da fasahar AI ɗin ta hanyar amfani da bayanan lafiyar mutane dubu ɗari huɗu – da ba a bayyana sunayensu ba – a Birtaniya da Denmark.

Zuwa yanzu ba a soma amfani da fasahar ba, sai dai ana sa ran yin amfani da ita wajen gano cutuka da wuri a mutanen da suka fi barazanar kamuwa da cutuka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fasahar AI ta gano cutar da za ta kama mutane a shekara 10 masu zuwa
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata