N50,000 aka biya ni don safarar harsasai zuwa Abuja – Matashi
Published: 12th, February 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Filato, ta kama wani matashi tare da wasu mutum uku kan zargin safarar harsasai daga Jos zuwa Abuja.
Matashin ya bayyana cewa ’yan ta’adda sun biya shi Naira 50,000 domin ya karɓo harsasai daga Jos zuwa Abuja.
Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum“Ni mazaunin Abuja ne.
“Ya tabbatar min babu wata matsala da zan fuskanta, amma a hanya jami’an tsaro suka kama mu ni da wasu mutum uku,” in ji matashin.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, yayin da yake holen waɗanda ake zargi, ya ce an kama su ne bayan samun rahoton sirri kan ayyukansu.
“Mun kama waɗanda ake zargin ne bayan samun sahihan bayanan sirri.
“Rundunar na ci gaba da bincike, kuma da zarar an kammala, za a miƙa su zuwa kotu domin fuskantar hukunci.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Harsasai Masu Safarar Makamai matsalar matsalar tsaro Safara
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
Wani jami’in ɗan sanda, SP Mustapha Garba Gumau, ya yi gamo ajalinsa a wani hatsarin mota yayin da ya rage aƙalla sa’a ɗaya a ɗaura masa aure.
Aminiya ta ruwaito cewa, ajali ya katse hanzarin jami’in ne a kan hanyar Gumau zuwa Magaman-Gumau da ke Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, inda za a ɗaura masa aure.
Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a KatsinaSP Gumau wanda hatsarin ya rutsa da shi da abokansa ya rasu ne da misalin ƙarfe 9 yayin da ake shirin ɗaura masa aure da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Asabar.
Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil ya fitar ta ce an tabbatar da rasuwar matashin da ke shirin angwancewa bayan an garzaya da shi asibiti.
Wakil ya ce jami’in ya rasu tare da wasu abokansa biyu da ke cikin wata mota ƙirar marsandi bayan sun yi karo da wata motar ƙirar Opel Vectra.
Sanarwar ta ambato Kwamishinan ’yan sandan Bauchi, CP Auwal Sani Omolori yana jajanta wa iyalan mamatan da kuma addu’ar mutuwa ta zamanto hutu a gare su.