HausaTv:
2025-09-17@21:52:22 GMT

 An Kashe Adadin Fararen Hular Da Bai Gaza 55 Ba A Arewacin Congo

Published: 11th, February 2025 GMT

Kungiyoyin da suke dauke da makamai sun kashe fararen hular da ba su gaza 55 ba a wani hari da su ka kai wa wasu kauyuka da sansanin ‘yan hijira a Arewacin DRC.

Mahukunta a yankin na Arewacin DRC sun ambaci cewa wasu masu dauke da makamai na kungiyar CODECO sun kai wa wasu kauyuka da suke yankin Djaiba hare-hare a gundumar Ituri a  jiya litinin da dare.

Bugu da kari masu dauke da makaman sun kai hari a cikin sansanin ‘yan hijira da suke a cikin wannan yankin kamar yadda shugaban sansanin Antoinnette Nzale ya fadawa manema labaru.

Ita dai kungiyar CODECO  gamayya ce ta kungiyoyin da suke dauke da makamai da su ka fito daga kabiluar Landu, manoma. Shekaru 4 da su ka gabata wannan kungiyar ta kai wasu hare-hare da ta kashe mutane 1,800 tare da jikkata wasu 500 a shekarar 2022.

MDD ta ce wannan harin za a iya daukarsa a matsayin  laifi akan bil’adama.

Nzake ya ce; sun kai wa dukkanin kauyukan da suke a yankin hari,” sannan ya kara da cewa; Dakarun tabbatar da zaman lafiya na MDD da ake kira; Monusco, tare da sojojin gwamnatin Congo, sun yi kokarin hana hare-hare amma masu dauke da makaman sun fi karfinsu. A watan Satumba da shekarar da ta kare ma, wannan kungiyar ta CODECO ta kai harin da ta kashe mutane 20 a garin Djugu, wanda shi ne garin da ta kai wa hari a wannan Litinin din da ta gabata.

A can gabashin kasar ta Congo ma dai  kungiyar M 23 mai samun goyon bayan Rwanda ta kwace iko da garin Goma mai muhimmanci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Rights Watch ta ce: Laifin da Isra’ila ta yi na kashe ‘yan jaridun Yemen babban ta’addanci ne

Kungiyar kare hakkin bil’ adama ta Human Rights Watch ta tabbatar da cewa: Harin da yahudawan sahayoniyya suka kai a ranar 26 ga watan Satumba kan ‘yan jaridun kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar ‘yan jarida sama da 30, laifi ne da ba za a iya kubutar da girman laifin kan wanda ya aikata ba.

A cikin rahoton baya-bayan nan, kungiyar ta fitar ta bayyana cewa, ta tattara bayanan harin da makiya yahudawan sahayoniyya suka kaddamar a ranar 10 ga watan Satumba kan hedkwatar kafafen yada labarai a kasar Yemen, kuma ta yi la’akari da wannan laifi a matsayin misali na hadarin da ‘yan jarida a Yemen da Palastinu ke fuskanta daga hare-haren wuce gona da iri na ‘yan sahayoniyya.

Kungiyar ta yi nuni da cewa harin da aka kai wa cibiyar ‘yan jaridu a ranar 26 ga watan Satumba a kasar Yemen, ya zo daidai da laifuffukan da yahudawan sahyuniya suka aikata a yankin Al-Jawf, wanda ya yi sanadin jikkatar fararen hula da dama, wadanda akasarinsu ‘yan jarida ne.

Wannan bayani ya karyata ikirarin makiya na cewa sun kai hari ne kawai a ginin ma’aikatar kula da dabi’u, kungiyar kare hakkin bil’adaman tana mai cewa faifan bidiyo da shaidun ganin ido na ‘yan kasar, sun tabbatar da cewa da gangan makiya yahudawan sahayoniyya suka kai hari kan hedkwatar ‘yan jaridun fararen hula.

An lura cewa: ” Unguwar da aka kai harin, wani yanki ne mai yawan jama’a da ke kusa da tsohon birnin Sana’a, wurin tarihi na UNESCO.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida September 16, 2025 Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza.
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa