An Kashe Adadin Fararen Hular Da Bai Gaza 55 Ba A Arewacin Congo
Published: 11th, February 2025 GMT
Kungiyoyin da suke dauke da makamai sun kashe fararen hular da ba su gaza 55 ba a wani hari da su ka kai wa wasu kauyuka da sansanin ‘yan hijira a Arewacin DRC.
Mahukunta a yankin na Arewacin DRC sun ambaci cewa wasu masu dauke da makamai na kungiyar CODECO sun kai wa wasu kauyuka da suke yankin Djaiba hare-hare a gundumar Ituri a jiya litinin da dare.
Bugu da kari masu dauke da makaman sun kai hari a cikin sansanin ‘yan hijira da suke a cikin wannan yankin kamar yadda shugaban sansanin Antoinnette Nzale ya fadawa manema labaru.
Ita dai kungiyar CODECO gamayya ce ta kungiyoyin da suke dauke da makamai da su ka fito daga kabiluar Landu, manoma. Shekaru 4 da su ka gabata wannan kungiyar ta kai wasu hare-hare da ta kashe mutane 1,800 tare da jikkata wasu 500 a shekarar 2022.
MDD ta ce wannan harin za a iya daukarsa a matsayin laifi akan bil’adama.
Nzake ya ce; sun kai wa dukkanin kauyukan da suke a yankin hari,” sannan ya kara da cewa; Dakarun tabbatar da zaman lafiya na MDD da ake kira; Monusco, tare da sojojin gwamnatin Congo, sun yi kokarin hana hare-hare amma masu dauke da makaman sun fi karfinsu. A watan Satumba da shekarar da ta kare ma, wannan kungiyar ta CODECO ta kai harin da ta kashe mutane 20 a garin Djugu, wanda shi ne garin da ta kai wa hari a wannan Litinin din da ta gabata.
A can gabashin kasar ta Congo ma dai kungiyar M 23 mai samun goyon bayan Rwanda ta kwace iko da garin Goma mai muhimmanci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
Shugaban kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’imKasim ya bayyana cewa, kungiyarsa tare da Sojojin kasar da kuma mutanen kasar ne zasu tabbatar da ci gaban kasar Lebanon a wannan halin da ake ciki.
Tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta nakalto sheikh Na’im kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Litinin, jawabinda kafafen yada labarai da damaa suka watsa kai tsaye.
Sheikh Qasim kasar Lebanon zata ci gaba da zama mai karfi idan gwamnatin kasar ta dakatar da hare-haren da HKI take ci gaba da kawowa a kan kasar, da kwato dukkan yankunan kasar da aka mamaye, har’ila yau da kuma ci gaba da hadin kai tsakanin masu gwagwarmaya, sojoji da kuma mutanen kasar.
Shugaban kungiyar ya jadda bukatar sake gina wuraren da HKI ta rusa a yankunan daban daban a kasar, ya ce gwamnatin kasar ta yi alkawalin zata sake gina wuraren da HKI ta rusa a yakin da hizbullah a baya-bayan nan.
Kuma ya ce rashin yin haka nuna bambanci ne a tsakanin mutanen kasar. Ya ce dangane da wadanda aka rusa gidajensu kungiyar ta bada kudaden haya ga 50,755 , sannan ta gyura wasu 332 da aka lalata, wanda duk aikin gwamnati ne ta yi hakan. Don haka akwai bukatar gwamnati ta aikata wajibin da ya hau kanta.