Gobara ta ƙone motoci da shaguna a wajen sayar da gas a Neja
Published: 9th, February 2025 GMT
Wata gobara da ta tashi a wajen sayar da gas a Sabon Wuse da ke Ƙaramar Hukumar Tafa a Jihar Neja, ta yi sanadin ƙonewar motoci da shaguna da kuma kayan abinci.
Lamarin ya faru ne a daren ranar Asabar lokacin da wata tanka ke sauke gas a wajen sayar da gas.
Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim mai suna Zarmalulu Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?Wutar ta ɗauki sa’o’i tana ci kafin isowar jami’an kashe gobara.
Wani mazaunin garin, Abdul Sabon-Wusa, ya ce bindigar ta girgiza yankin, inda mutane suka firgita suka fito daga gidajensu domin neman mafaka.
Wutar ta kuma bazu zuwa wani gidan mai, inda ta ƙone shaguna da motoci da aka ajiye.
“Muna godiya ga Allah ba a rasa rai ba, kuma ba a samu wanda ya jikkata ba.
“Idan hakan ta faru da rana lokacin da mutane ke kasuwancinsu, da wani babban iftila’in ne zai faru,” in ji shi.
Ya ce hayaƙin gobarar ya tashi sama sosai har ana iya ganinsa daga sassa daban-daban na garin, wanda ke nuna yadda wutar ta yi ƙamari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Wajen Sayar Gas
এছাড়াও পড়ুন:
Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.
Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a ChinaUwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.
Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.
Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.