Sojojin Sudan Suna Samun Nasarar ‘Yantar Da Garuruwan Kasar Daga Mamayar ‘Yan Tawaye
Published: 7th, February 2025 GMT
Majiyoyin sojin Sudan sun sanar da cewa: Sun sake samun nasarar kwace iko da babban birnin kasar Khartoum
Majiyoyin sojin Sundan sun sanar da cewa: Cikin dan gajeren lokaci sun samu nasarar sake kwace iko da birnin Khartoum fadar mulkin kasar daga mamayar dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, bayan da suka yi birnin kawanya daga bangarori hudu.
A nata bangaren, Ma’aikatar yada labaran Sudan ta zargi bangarorin waje da jagorantar gudanar da fadace-fadacen da ‘yan tawayen dakarun kai daukin gaggawa ke yi don samun damar cin gajiyar albarkatun kasar, idan ‘yan tawaye suka yi nasara.
Rayuwa ta fara inganta a birnin Omdurman kuma kasuwanni sun fara farfadowa, inda jama’a suke komawa ci gaba da harkokinsu na yau da kullum ciki har da garuruwan Kassala da Port Sudan tare da tafiye-tafiye zuwa birnin Khartoum fadar mulkin kasar, tare da cewa an fara aikin sake gina kasar ayankunan da aka samu kwanciyar hankali, amma har yanzu ana cikin damuwa da fargaba a birnin Khartoum sakamakon hare-haren bama-bamai da dakarun kai daukin gaggawa ke kai wa ta sama musamman kan asibitoci da kasuwanni.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce matakin da gwamnatin Isra’ila ta dauka a kan kasar tamkar shelanta yaki ne.
Araghchi ya bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ya aikewa babban sakatare na MDD da kuma shugaban kwamitin sulhu bayan da Isra’ila ta kai munanan hare-hare kan wuraren soji da cibiyoyin nukiliya da kuma wuraren zama wanda ya yi sanadiyar mutuwar wasu manyan kwamandojin dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), masana kimiyyar nukiliya da fararen hula na iran.
“Wadannan ayyuka na zalunci ba wai kawai sun zama babban cin zarafi ne ga ‘yancin kan kasar Iran a matsayinta na mamba mai cin gashin kanta a Majalisar Dinkin Duniya ba, amma kamar yadda dokokin kasa da kasa da dokokin jin kai na duniya, ciki har da yarjejeniyar Geneva, suka tanada wannan na daga cikin ayyukan wuce gona da iri da laifukan yaki.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya sauke nauyin da ke wuyansa, ya yi kakkausar suka ga wannan ta’addanci tare da daukar matakin gaggawa kan Isra’ila.
Ya kara da cewa “Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki da cikakkiyar azama wajen kare ‘yancinta, al’ummarta da kuma tsaron kasarta. Wannan wani hakki ne da ba za a iya tattaunawa da shi ba.”
Daga cikin hare-haren da ta kai, Isra’ila ta kai hari kan Cibiyar Nukiliya ta Natanz da ke tsakiyar kasar Iran, wadda ke aiki karkashin cikakken kulawar Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA), in ji shi.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi gargadin cewa hare-haren ta’addanci na gwamnatin Tel Aviv na jefa rayuwar fararen hular Iran cikin hadari tare da haifar da barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.