Amurka Za Ta Fice Daga Hukumar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD
Published: 4th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donald Trump zai rattaba hannu kan wasu takardun bayar da umarni na bangaren zartaswa, game da janyewar Amurka daga hukumar kare hakkin bil’adama ta majalisar dinkin duniya (UNHRC) da kuma dakatar da bayar da tallafi ga hukumar bayar da agaji ga Falasdinu ta majalisar dinkin duniya (UNRWA).
Wata kafar yada labarai ta cikin gida a Amurka ta bayar da rahoton haka, daga wata majiya ta hukuma a fadar White House.
Yau talata kuma Trump na ganawa da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, wanda ya dade yana sukar hukumar ta bayar da agaji ga Falasdinu ta UNRWA.
A lokacin wa’adin farko na mulkin Trump a watan Yunin 2018, Amurka ta fice daga hukumar kare hakkin bil’adama ta majalisar dinkin duniya, tana mai cewa hukumar ta bayar da damar zama mamba a cikinta ga kasashen da ba su cancanta ba, kuma ta kafa kahon zuka da kuma nuna muguwar kiyayya mara iyaka ga Isra’ila.
Tun dai bayan hawansa mulkin AMurka a karo na Biyu Trump ya sanar da soke yarjejeniyoyi da dama da kuma janye kasarsa daga wasu kungiyoyi na kasa da kasa.
Na baya baya nan ita ce hukumar lafiya ta Duniya, WHO, da kuma soke tallafin da Amurka ke baiwa kasashen ketare in ban da na kawar kasar Isra’ila da kuma Masar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.
Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.
Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.
NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau UkuA kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.
Domin sauke shirin, latsa nan