Aminiya:
2025-11-02@19:36:14 GMT

Likitoci sun tsunduma yajin aiki a fadin Najeriya

Published: 12th, September 2025 GMT

Kungiyar Likitocin Masu Neman Kwarewa ta Najeriya (NARD) ta umurci mambobinta da su dakatar da aiki a dukkan asibitocin gwamnati da ke fadin Najeriya daga yau Juma’a.

Wannan mataki ya biyo bayan karewar wa’adin sa’o’i 24 da kungiyar ta bai wa Gwamnatin Tarayya don cika bukatunsu da ba a biya ba.

Wa’adin ya biyo bayan karewar wani wa’adin na kwanaki 10 da ya kare a ranar 10 ga Satumba ba tare da an biya wa likitocin bukatun nasu ba.

Ambaliyar ruwa ta tsayar da ababen hawa cak a tsakiyar birnin Abuja Jonathan ya tattauna da Peter Obi kan tsayawa takara a 2027

A ranar daya ga watan Satumba, NARD ta gargadi gwamnati cewa za ta fara yajin aikin sai baba ta gani idan ba a saurari bukatunsu ba cikin kwanaki 10.

Likitocin, wadanda su ne suka fi yawa a asibitocin koyarwa da asibitocin kwararru, sun sha shiga yajin aiki a shekarun baya saboda matsaloli kamar su rashin biyan albashi, rashin jin dadin aiki da kuma yanayin aiki mara kyau.

Shugaban NARD, Dr. Tope Osundare, ya shaida wa Aminiya a ranar Alhamis cewa sabon wa’adin ya fito ne daga taron sa’o’i shida da Majalisar Zartarwa ta Kasa (NEC) ta kungiyar ta gudanar ta bidiyo a ranar Laraba.

Aminiya ta rawaito cewa likitocin na bukatar a biya su kudin horar da likitocin gida na shekarar 2025 da aka rike musu, sai bashin watanni biyar na karin albashi da aka yi tsakanin kashi 25 zuwa 35 cikin dari, da sauran bashin albashi da suka dade suna bi.

Sauran bukatun sun hada da biyan bashin kudin kayan aiki na shekarar 2024, biyan kudin kwararru cikin lokaci, da dawo da amincewa da takardun digiri na biyu na Afirka ta Yamma.

Osundare ya ce duk da alkawarin da gwamnati ta yi wa kungiyarsu na magance matsalolin, sun dage sai an dauki matakin cika su nan take kafin su yarda su koma aiki.

Ya ce: “Gwamnatin Tarayya ta kira mu jiya kuma ta yi alkawarin magance matsalolinmu.

“Mun yi taronmu, kuma bayan tattaunawa na sa’o’i shida, mun yanke shawarar bai wa gwamnati sa’o’i 24 don tabbatar da biyan kudin MRTF ga wadanda suka cancanta, MDCN ta sabunta takardun mambobinmu, da kuma magance sauran bukatunmu.

“Idan babu wani abu da ya faru kafin karshen yau (Alhamis), za mu fara yajin aiki nan take gobe (Juma’a).

“Gwamnati ta gaggauta daukar mataki kan bukatun da ke gabanta.”

A safiyar Juma’a, Osundare ya tabbatar wa Daily Trust cewa yajin aikin ya fara.

“Abin takaici, ba a cika ko da daya daga cikin bukatun da muka gabatar cikin wa’adin sa’o’i 24 ba, kuma yajin aikin ya fara a safiyar nan kamar yadda NEC ta umurta,” in ji shi a cikin gajeren sakon da ya tura wa wakilinmu.

Da aka tambaye shi ko yajin aikin na gargadi ne, sai ya amsa da cewa, “Za mu sake duba lamarin bayan Gwamnatin Tarayya ta dauki matakin da ya dace.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: NARD Yajin aiki yajin aikin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar

Daga Usman Muhammad Zaria 

 

Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.

Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.

Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.

Ya ce an tsara wannan asusu  ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.

Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.

Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin  ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.

Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a  wuraren.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar