Aminiya:
2025-09-17@21:50:13 GMT

Majalisar Dinkin Duniya ta yi alla-wadai da harin Bama

Published: 9th, September 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya ta yi alla-wadai da wani harin da ’yan ta’adda suka kai a garin Darul Jamal, da ke karamar hukumar Bama a Jihar Borno.

Mohamed Malick Fall, Babban Jami’i mai Kula da Ayyukan jinkai na Majalisar a Nijeriya, ya bayyana matukar bakin cikinsa kan lamarin, wanda ya faru a yammacin ranar Jumma’a, 5 ga watan Satumba.

“Ina matukar bakin ciki da rahoton kisan da aka yi wa sojoji da fararen hula da dama a ranar Juma’a a kauyen Dara Jamal,” in ji Fall.

Rahotannin farko sun nuna cewa an kashe fararen hula fiye da 50, inda ake zargin an yi garkuwa da wadanda ba a san adadinsu ba.

Kazalika, bayanai sun nuna mutane da dama sun gudu daga muhallansu, sannan an kone gidaje fiye da 20 kurmus a lokacin harin.

Jami’in, a madadin ofishin majalisar a Nijeriya, ya kuma mika saƙon ta’aziyya ga iyalan wadanda harin ya shafa, gwamnati, da kuma al’ummar Jihar Borno, tare da yi wa wadanda suka ji rauni fatan samun sauki cikin gaggawa.

“Ina kira ga hukumomin tsaro da su kamo wadanda suka aikata wannan ɗanyen aikin. Ina kuma kira da a gaggauta sakin duk wadanda aka sace,” in ji shi.

Jami’in ya bayyana lamarin a matsayin wani mummunan tunatarwa kan yadda tashe-tashen hankula da rashin tsaro ke ci gaba da addabar Jihar Borno a duk shekara.

Rahotanni sun nuna cewa, an dade ana kashe fararen hula da ‘yan gudun hijira, manoma, matafiya, da ‘yan kasuwa a irin wadannan hare-haren.

Dabarun da ‘yan ta’adda ke amfani da su sun hada da bama-bamai da kai harin kunar bakin wake, da dai sauran munanan hanyoyi.

Bugu da kari, Fall ya lura cewa jihohin Adamawa da Yobe da ke da makwabtaka da Jihar Borno ba su tsira ba, inda aka kai hare-hare a cibiyoyin kiwon lafiya da kuma kasuwanni.

Majalisar Dinkin Duniya ta sake jaddada aniyar ta na ci gaba da tallafawa wadanda rikici ya shafa a Nijeriya, a kokarin da gwamnatin ke yi na dakile ayyukan ‘yan ta’adda..

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.

A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.

Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.

Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.

“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.

Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.

Gwamnan ya kuma sake jaddada  cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.

Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)