Majalisar Dinkin Duniya ta yi alla-wadai da harin Bama
Published: 9th, September 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya ta yi alla-wadai da wani harin da ’yan ta’adda suka kai a garin Darul Jamal, da ke karamar hukumar Bama a Jihar Borno.
Mohamed Malick Fall, Babban Jami’i mai Kula da Ayyukan jinkai na Majalisar a Nijeriya, ya bayyana matukar bakin cikinsa kan lamarin, wanda ya faru a yammacin ranar Jumma’a, 5 ga watan Satumba.
“Ina matukar bakin ciki da rahoton kisan da aka yi wa sojoji da fararen hula da dama a ranar Juma’a a kauyen Dara Jamal,” in ji Fall.
Rahotannin farko sun nuna cewa an kashe fararen hula fiye da 50, inda ake zargin an yi garkuwa da wadanda ba a san adadinsu ba.
Kazalika, bayanai sun nuna mutane da dama sun gudu daga muhallansu, sannan an kone gidaje fiye da 20 kurmus a lokacin harin.
Jami’in, a madadin ofishin majalisar a Nijeriya, ya kuma mika saƙon ta’aziyya ga iyalan wadanda harin ya shafa, gwamnati, da kuma al’ummar Jihar Borno, tare da yi wa wadanda suka ji rauni fatan samun sauki cikin gaggawa.
“Ina kira ga hukumomin tsaro da su kamo wadanda suka aikata wannan ɗanyen aikin. Ina kuma kira da a gaggauta sakin duk wadanda aka sace,” in ji shi.
Jami’in ya bayyana lamarin a matsayin wani mummunan tunatarwa kan yadda tashe-tashen hankula da rashin tsaro ke ci gaba da addabar Jihar Borno a duk shekara.
Rahotanni sun nuna cewa, an dade ana kashe fararen hula da ‘yan gudun hijira, manoma, matafiya, da ‘yan kasuwa a irin wadannan hare-haren.
Dabarun da ‘yan ta’adda ke amfani da su sun hada da bama-bamai da kai harin kunar bakin wake, da dai sauran munanan hanyoyi.
Bugu da kari, Fall ya lura cewa jihohin Adamawa da Yobe da ke da makwabtaka da Jihar Borno ba su tsira ba, inda aka kai hare-hare a cibiyoyin kiwon lafiya da kuma kasuwanni.
Majalisar Dinkin Duniya ta sake jaddada aniyar ta na ci gaba da tallafawa wadanda rikici ya shafa a Nijeriya, a kokarin da gwamnatin ke yi na dakile ayyukan ‘yan ta’adda..
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Borno
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Isra’ila ba za ta kai hari kan Iran ba sai da goyon bayan Amurka
Ministan harkokin wajen Iran Seyyed Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya ba za ta kaddamar da yaki kan Jamhuriyar Musulunci ba tare da samun wata kariya daga Amurka ba. Ya kara da cewa, Iran ta gudanar da yakin kwanaki goma sha biyu da wannan gwamnati mai wuce gona da iri, kuma ta hana ta ci gaba da mummunar manufarta ta mamaya a yankin.
A wata hira da ya yi da gidan talabijin na Al- Jazeera, Araqchi ya yi nuni da cewa: Gwamnatin masu wuce gona da iri ta yi kokarin fadada yakin zuwa yankin ta hanyar kai hari kan cibiyoyin man fetur na Iran, amma Iran ta yi nasarar shawo kan yakin kuma ta hana aukuwan hakan.”
Yayin da yake fayyace shirye-shiryen Jamhuriyar Musulunci ta Iran na tattaunawa don kawar da damuwar da ake da ita game da shirin makamashin nukiliyarta na zaman lafiya, Ministan Harkokin Wajen ya jaddada cewa: “Sun shirya wa duk wani abu da zai faru kuma suna tsammanin duk wani hali mai tsauri daga ‘yan sahayoniyya.” Ya bayyana cewa Iran ta samu kwarewa mai yawa daga yakin da ta yi kwanan nan kuma ta samu damar gwada makamai masu linzaminta a wannan yaƙi na gaske.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci