Aminiya:
2025-09-17@21:53:53 GMT

An fara samun masu zawarcin kujerar Firaministan Japan

Published: 8th, September 2025 GMT

An fara samun masu zawarcin kujerar Firaministan Japan da ya yi murabus, inda tsohon Ministan Harkokin Waje ya bayyana takarar neman kujerar mai tasiri a kasar wadda take sahun gaba na kasashe masu arziki a duniya.

Tsohon Ministan Harkokin Wajen kasar Japan, Toshimitsu Motegi ya zama mutum na farko da ya nemi ’yan majalisar dokoki na jam’iyya mai mulki ta Liberal Democratic Party (LDP) su ba shi damar zama sabon Firaminista, domin ya maye gurbi Firamnista Shigeru Ishiba mai barin gado wanda ya bayyana yin murabus daga kan mukamin.

Sojoji sun kashe kasurgumin dan ta’adda da yaransa 5 a Kogi Yiwuwar yajin aikin direbobin tankar mai kan rikicin Matatar Dangote

Aminiya ta ruwaito cewa a jiya Lahadi ce Firaministan Japan, Shigeru Ishiba, ya sanar da murabus dinsa a matsayin shugaban jam’iyyar Liberal Democratic Party (LDP), watanni kaɗan bayan jam’iyyarsa ta sha mummunan kaye a zaɓen watan Yuli.

Ishiba ya sanar da matakin duk da cewa a baya ya yi ƙoƙarin kaucewa matsin lambar ‘yan jam’iyyarsa da ke neman ya sauka sakamakon rashin nasarar zaɓen, inda ya dage cewa yana son tabbatar da yarjejeniyar haraji da ƙasar ta ƙulla da Amurka ta fara aiki yadda ya kamata.

“Tun da Japan ta sanya hannu kan wannan yarjejeniya, kuma shugaban Amurka ya rattaba hannu a matsayin doka, mun tsallake babban ƙalubale,” in ji shi.

“Lokaci ya yi da zan miƙa wa sabon jini tutar shugabanci,” ya ƙara da cewa.

Duk da murabus ɗinsa daga shugabancin jam’iyyar, Ishiba zai ci gaba da zama Firaminista har zuwa lokacin da za a gudanar da zaɓen cikin gida domin zaɓen sabon shugaban LDP.

Gidan Talabijin na Al-Jazeera ya ruwaito cewa wannan mataki ya ƙara jefa Japan, wacce ita ce ƙasa ta huɗu mafi girman tattalin arziƙi a duniya, cikin ruɗanin siyasa.

Tun bayan hawansa mulki a watan Oktoba da ya gabata, ɗan siyasar mai shekara 68 ya gamu da manyan ƙalubalai da suka yi sanadin kawar da rinjayen ’yan jam’iyyarsa a majalisun biyu na ƙasar.

Rashin nasarar, wanda aka danganta shi da ƙorafin jama’a kan tsadar rayuwa, ya sa gwamnatin Ishiba ta kasa aiwatar da manufofinta yadda ta tsara.

Yayin da ƙasar ke ƙara faɗawa cikin ruɗanin siyasa, manyan ‘yan jam’iyyarsa musamman daga bangaren ’yan ra’ayin mazan jiya sun matsa masa lambar yin murabus, waɗanda suka ɗora masa alhakin rashin nasara a zaɓen majalisar dattawa na Yuli.

Rahotanni sun ce Ministan Aikin Noma na Japan tare da tsohon Firaministan sun gana da shi a daren ranar Asabar domin shawartarsa da ya yi murabus.

A taron manema labarai da ya kira ranar Lahadi, Ishiba ya tabbatar da murabus ɗinsa, tare da bayyana cewa ya fara shirye-shiryen neman wanda zai gaje shi.

Yayin da ƙasar ke ƙara nutsewa cikin rudanin siyasa, manyan ‘yan jam’iyyarsa musamman daga bangaren ’yan ra’ayin mazan jiya sun matsa masa lamba da ya sauka, suna zarginsa da alhakin sakamakon zaben majalisar dattawa na Yuli.

Rahotanni sun ce Ministan Aikin Noma na Japan tare da tsohon Firayim Minista sun gana da shi a ranar Asabar da dare don shawarce shi ya sauka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan jam iyyarsa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

 

Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara