Boko Haram sun kashe gomman mutane da sojoji a ƙauyen Borno
Published: 6th, September 2025 GMT
Ana zargin mayaƙan Boko Haram sun kai hari ƙauyen Darul Jamal da ke Karamar Hukumar Bama, a Jihar Borno, inda suka kashe gomman mutane da sojoji.
Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 9 na daren ranar Juma’a.
’Yan bindiga sun kashe mutum 7 a Katsina Yadda makarantu ke tatsar kuɗaɗe daga iyayen ɗalibaiMutane da hukumomin tsaro sun tabbatar da aukuwar harin.
A kwanakin baya, Gwamnan Jihar, Babagana Umara Zulum, ya mayar da wasu mutane ƙauyen.
Shekaru da dama suna zaman ’yan gudun hijira a sansanoni daban-daban kafin a dawo da su.
Wani daga cikin mazauna yankin ya ce: “Rana ce mai matuƙar baƙin ciki. Ɗana da ɗan uwana sun mutu.
“Mun kirga gawarwaki 63 kuma mutane da dama sun jikkata. An tafi da wasu zuwa asibitoci a Maiduguri, yayin da wasu ke karɓar magani a Bama.”
Rahotanni sun nuna cewa maharan sun ƙone gidaje da motoci.
Yawancin kashe-kashen sun faru ne a kusa da makarantar da ’yan gudun hijira, tashar mota, da kuma gidaje.
Wani mazaunin yankin ya ce maharan sun kai harin cikin shiri, inda suka kai farmaki wuraren da mutane suka taru.
Sun buɗe wa ’yan gudun hijira, ma’aikata, direbobi, da jami’an tsaro wuta.
Ya ƙara da cewa ’yan ta’addan ba sa son mutane su zauna a garin, shi ya sa suka kai harin.
Hukumomi har yanzu suna faɗi adadin waɗanda suka rasu, yayin da wasu da suka ji munanan raunuka ke rasuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram hari
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’uSauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.
An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.
Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.
Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.
Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.