Aminiya:
2025-11-02@16:52:01 GMT

Matasa sun kashe ’yan bindiga 6 sun sha alwashin kare kansu

Published: 4th, September 2025 GMT

Matasan Ƙaramar hukumar Shagari sun kashe wasu ’yan bindiga shidda da ake zargin suna cikin waɗanda suka addabi yankin Ƙaramar hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.

Wani matashi ya yi wa wakilinmu bayanin yadda lamarin ya faru ya ce, ’yan bindigar sun zo kan Jakuna a cikin dajin da ba kowa, a safiyar Alhamis inda  mutane da ke tsare gari ba su watse ba suka gansu a nan ne suka yi masu ƙofar raggo, suna tare da shanun da suka sata da wasu baƙin shanu.

Mai taɓin hankali ta haihu a tsakiyar kasuwa a Oyo Hatsarin Jirgin Ruwa: Adadin waɗanda suka rasu ya kai 60 a Neja

“An gansu su bakwai an kashe shidda daga cikinsu an bar guda raye aka ɗaure shi,  su shiddan ga su a kwance ba rai, mutane sun yanke hukuncin kare kansu don sun ga gwamnatin Sakkwato ba da gaske take kan lamarin tsaro ba.” A cewarsu

Shugaban Ƙaramar hukumar Shagari, Alhaji Muhammad Maidawa ya ce da safiyar Alhamis labari ya zo masa akwai wasu baƙin Fulani jajaye da aka afkawa a garin Shagari, amma komai ya lafa sojoji sun kwantar da tarzomar.

Kan maganar adadin waɗanda aka kashe ya ce har yanzu jami’an tsaro ba su gama tantancewa ba, in sun ƙare za su sanar da shi ya ba da bayani.

Matasa a ƙarƙashin Ƙungiyar Shagari Youths a Ƙaramar hukumar Shagari ta jihar sun yi barazanar ɗaukar matakin kare kansu sakamakon taɓarɓarewar tsaro a yankin.

Matasan sun kuma zargi gwamnati da sakaci duk da hare-haren ’yan bindiga da ake ta fama da su tare da ƙorafe-ƙorafen jama’a.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin Ƙungiyar ta hannun Bello Bala Shagari, ya bayyana cewa matasan sun yanke wannan shawara ne a wani taro na intanet da suka gudanar ranar Laraba.

Ya ce: “Da dama sun bayyana cewa, gwamnati ta gaza wajen cika alhakin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Saboda haka, kare kai yanzu shi ne kaɗai zaɓin da ya rage.”

Ya ƙara da cewa, matasan sun yanke shawarar ɗaukar duk wani mataki da ya dace domin kare kansu daga cin zarafi da hare-haren ’yan bindiga.

Sai dai Shagari ya bayyana cewa, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Yabo/Shagari, Umar Yusuf-Yabo, ya yi kira da a yi haƙuri, a bi doka tare da samun ƙarin shawarwari.

Duk da ya nuna fahimtar takaicin da matasan ke ciki, ya roƙi gwamnati da ta hanzarta ɗaukar mataki domin daƙile abin da ya ce na iya “rikiɗewa zuwa barazana mai girma.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ƙungiyar Shagari Youths Sakkwato Shagari Ƙaramar hukumar Shagari yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa

Manajar  ofishin na NIWA,  da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.

Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.

“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.

“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.

Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA,  Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa  da ke a sassan kasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Labarai Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari