Matasa sun kashe ’yan bindiga 6 sun sha alwashin kare kansu
Published: 4th, September 2025 GMT
Matasan Ƙaramar hukumar Shagari sun kashe wasu ’yan bindiga shidda da ake zargin suna cikin waɗanda suka addabi yankin Ƙaramar hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.
Wani matashi ya yi wa wakilinmu bayanin yadda lamarin ya faru ya ce, ’yan bindigar sun zo kan Jakuna a cikin dajin da ba kowa, a safiyar Alhamis inda mutane da ke tsare gari ba su watse ba suka gansu a nan ne suka yi masu ƙofar raggo, suna tare da shanun da suka sata da wasu baƙin shanu.
“An gansu su bakwai an kashe shidda daga cikinsu an bar guda raye aka ɗaure shi, su shiddan ga su a kwance ba rai, mutane sun yanke hukuncin kare kansu don sun ga gwamnatin Sakkwato ba da gaske take kan lamarin tsaro ba.” A cewarsu
Shugaban Ƙaramar hukumar Shagari, Alhaji Muhammad Maidawa ya ce da safiyar Alhamis labari ya zo masa akwai wasu baƙin Fulani jajaye da aka afkawa a garin Shagari, amma komai ya lafa sojoji sun kwantar da tarzomar.
Kan maganar adadin waɗanda aka kashe ya ce har yanzu jami’an tsaro ba su gama tantancewa ba, in sun ƙare za su sanar da shi ya ba da bayani.
Matasa a ƙarƙashin Ƙungiyar Shagari Youths a Ƙaramar hukumar Shagari ta jihar sun yi barazanar ɗaukar matakin kare kansu sakamakon taɓarɓarewar tsaro a yankin.
Matasan sun kuma zargi gwamnati da sakaci duk da hare-haren ’yan bindiga da ake ta fama da su tare da ƙorafe-ƙorafen jama’a.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin Ƙungiyar ta hannun Bello Bala Shagari, ya bayyana cewa matasan sun yanke wannan shawara ne a wani taro na intanet da suka gudanar ranar Laraba.
Ya ce: “Da dama sun bayyana cewa, gwamnati ta gaza wajen cika alhakin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Saboda haka, kare kai yanzu shi ne kaɗai zaɓin da ya rage.”
Ya ƙara da cewa, matasan sun yanke shawarar ɗaukar duk wani mataki da ya dace domin kare kansu daga cin zarafi da hare-haren ’yan bindiga.
Sai dai Shagari ya bayyana cewa, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Yabo/Shagari, Umar Yusuf-Yabo, ya yi kira da a yi haƙuri, a bi doka tare da samun ƙarin shawarwari.
Duk da ya nuna fahimtar takaicin da matasan ke ciki, ya roƙi gwamnati da ta hanzarta ɗaukar mataki domin daƙile abin da ya ce na iya “rikiɗewa zuwa barazana mai girma.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ƙungiyar Shagari Youths Sakkwato Shagari Ƙaramar hukumar Shagari yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
Aƙalla masallata 40 ’yan bindiga suka sace a wani masallaci da ke Gidan Turbe a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara da safiyar wannan Litinin.
Majiyoyi sun ce an yi awon gaba da masallatan ne zuwa dazukan Gohori da ke yankin Tsafe.
Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a LegasWannan harin dai kai tsaye masu ruwa da tsaki na kallonsa a matsayin kawo ƙarshen yarjejeniyar sulhu tsakanin ’yan bindigar da mahukuntan jihohin Zamfara da Katsina.
A baya-bayan nan ne jihohin Katsina da Zamfara suka ƙulla yarjejeniyar sulhu tsakaninsu da ’yan bindigar da suka addabi al’ummar jihohin arewa maso yammacin Najeriyar.
Yarjejeniyar sulhu da aka cimma a dajin Wurma ta samu halartan manyan ’yan bindiga irinsu Alhaji Usman Kachalla Ruga da Muhindinge da Yahaya Sani ( Hayyu ) da kuma Shu’aibu.
A ɓangaren mahukunta, akwai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi da kuma shugaban ƙaramar hukuma Babangida Abdullahi Kurfi.
’Yan bindiga sun saki wasu mutane da suke garkuwa da su a lokacin yarjejeniyar sulhun, tare da barin al’umma zuwa gonakinsu ba tare da wata fargaba ko tsangwama.
To sai dai kuma, ƙasa da wata guda bayan cimma wannan yarjejeniya, rahotanni sun ce ’yan bindiga sun kutsawa wani ƙauye a Zamfara tare da awon gaba da masallata.
Shaidun gani da ido sun ce, maharan sun yi wa masallacin ƙawanya da misalin ƙarfe 5:30 na safe, daidai lokacin da jama’a ke sallar asuba.