NAF ta hallaka ’yan ta’adda 15 a dajin Sambisa
Published: 4th, September 2025 GMT
Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF), ta kashe ’yan ta’adda sama da 15 a wani harin jiragen yaƙi da aka kai dajin Sambisa, da ke Jihar Borno.
Mai magana da yawun NAF, Ehimen Ejodame, ya ce an ƙaddamar da harin ne a ranar Laraba karkashin Operation Haɗin Kai.
Umar FK ya fice daga PDP zuwa APC da magoya bayansa a Gombe Kwankwaso zai iya komawa APC – Abdulmumin KofaYa ce sun samu bayanan sirri da suka nuna cewa mayaƙan da ke da hannu a hare-haren a yankin Bitta sun ɓuya a wajen.
Ya ce hare-haren sun lalata maɓoyar ’yan ta’addan tare da raunata da dama da cikinsu.
Ejodame ya ƙara da cewa wannan ya nuna ƙwarewar NAF da kuma jajircewarta wajen tallafa wa sojojin ƙasa da kare rayukan ’yan Najeriya.
“Duk nasarar da ake samu tana ƙara kusantar da Najeriya wajen samun zaman lafiya ta hanyar rushe hanyar sadarwar ’yan ta’adda,” in ji shi.
Hakazalika, a farkon makon nan dakarun Operation Haɗin Kai tare da tallafin sojin sama sun kashe ’yan ta’adda 20 a Jihar Borno da Yobe.
Har ila yau, sun kama wasu da ke taimaka musu da kuma lalata wasu bama-bamai da suka samu a wajensu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Hallakawa Operation Haɗin Kai yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.
Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.
Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.
NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau UkuA kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.
Domin sauke shirin, latsa nan