Dantsoho ya sanar da cewa, tun lokacin da aka yi aikin Tashoshin Jiragen Ruwa na Tin Can Island shekaru 48 da kuma aikin Tashar Jiragen Ruwa ta and Apapa 103 a shekaru da suka gabata, babu wani yunkuri da aka yi, na gyransu ko kuma kara daga darajarsu.

 

Shugaban ya kuma koka kan yadda aka shafe wadannan shekarun masu yawan gaske, ba tare da an yi masu wani gyara ba.

 

Ya buga misali da kananan Tashoshin Jiragen Ruwa na kasasehe kamar na Togo, Côte d’Iboire da Ghana, wanda suka kasance, Tashoshin Jiragen Ruwa da manyan Jiragen Ruwa ke sauka.

A cewar Shugaban irin lalacewar da kayan aiki a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar suka yi, abu ne, da ya wuce kima, wanda hakan ya sanya, sauran Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma, har ta kai ga suna yin gasa na kasar nan, wajen gudanar da hada-hadar kasuwancinsu.

“Abokan gasar mu kamar Tashoshin Jiragen Ruwa na Lome, Cotonou, Abidjan da Tema, na yin amfani da damar halin da Tashoshin Jiragen mu suke a ciki ne, suke more damar gudanar da hada-hadarsu, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Shugaban.

“Dangane da bayaan da aka samu na duniya, Nijeriya ta kasance kasa, da ke da karfin tattalin ariziki kuma mai alumma da dama a fadin nahiyar Afirka, amma har zuwa yau, Abidjan da Lome na karbar saukar manyan Jiragen Ruwa masu yawa, fiye da wadanda suke sauka a Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas, “ Acewar Dantsoho.

Shugaban ya sanar da cewa, ya zama wajibi, mu tabbatar da mun ciki wannan gibin da ake da shi, a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

Ya bayyana cewa, da zarar an samar da sauran kayan aikin da suka hada da kimiyyar zamani da sauransu, Tashoshin za a samu karin damar saukar manyan Jiragen Ruwan.

Ya kuma koka kan karancin kayan aiki na saukar Jiragen a Tashoshin, wanda hakan ya sanya, Hukumar ta NPA ke zuba sabbin kayan aikin ciki har da manyan motocin janyewa da sauransu.

Sai dai, ya sanar da a zagon farko na shekarar 2026 ake sa ran isowar kayan zuwa cikin kasar nan

Ya ci gaba da cewa, hakan ne ke shafar Matatar Mai ta Dangote da ke a Lekki inda ya yi nuni da cewa, Hukumar ta NPA kuma, ba ta irin kayan aikin da za su iya janyo wadannan Tankokin Man din.

Dantsoho ya sanar da cewa, Gwamnatin Tarayya ta kafa wani waje domin samar da saukin gudanar da ayyukan Matatar Mai ta Dangote, inda aka warewa hukumomin Gwamnati guda 16 wasu gurare, a cikin harabar Hukumar NPA, wanda hakan ya bai wa NPA damar tara kudaden shiga da suka kai sama da Naira biliyan 25, tun daga watan Okutobar 2024, zuwa yau.

Ya ce, NPA na goyon bayan sauye-sauyen da Gwamnatin ke ci gaba da yi, a fannin tattalin arzikin kasar, wanda hakjan zai janyo hankulan masu son zuba hannun jari a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar

Shi kuwa Aminu Umar, Shugaban Cibiyar a jawabinsa na maraba a wajen taron ya jaddada cewa, kirkiro da Ma’aikatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa na Teku, hakan na da matukar mahimmanci a bangaren shigo da kaya daga waje da kuma fitar da su, daga cikin kasar zuwa ketare.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Jiragen Ruwan ya sanar da

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kama wani ɗan ƙasar Indiya tare da wasu mutane uku bisa zargin shigo da ƙwayoyin Tramadol da aka ƙiyasta darajarsu ta kai naira biliyan uku (N3bn) zuwa cikin ƙasar.

A cewar NDLEA, wannan shi ne kamen ƙwayoyi mafi girma da hukumar ta yi a cikin shekarar nan, lamarin da ke nuna yadda safarar miyagun ƙwayoyi ke ƙaruwa a ƙasar.

Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa jami’anta sun kama mutanen ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas, bayan sun samu bayanan sirri da suka taimaka wajen gano su.

NDLEA ta bayyana cewa ƙwayoyin Tramadol ɗin da aka gano an shigo da su ne cikin kwalaye a matsayin maganin multivitamins, yayin da ake ƙoƙarin fitar da su daga filin jirgin a wasu manyan motoci.

“Ƙwayoyin da aka kama ba su da wata alaƙa da amfani na lafiya, waɗanda aka shigo da su a ɓoye a matsayin maganin rage kasala da ƙara kuzari (multivitamins),” in ji sanarwar NDLEA.

Rahotanni sun nuna cewa a da likitoci na bayar da Tramadol ne don rage zafi da raɗaɗin ciwo, amma yanzu ta zamo annoba musamman a tsakanin matasa, wadda ke haddasa mummunan maye da illa ga lafiya.

Hukumar ta nuna damuwa game da yadda yawan masu amfani da Tramadol ke ƙaruwa ba wai a Najeriya kaɗai ba, har ma a wasu ƙasashen Afirka, duk da illolin da ƙwayar ke haddasawa, kamar matsalolin taɓin hankali ko ma rasa rai gaba ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin
  • Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)