Kotu ta daure dan Shugaban Equatorial Guinea kan sayar da jirgin saman kasar
Published: 28th, August 2025 GMT
Wata kotu a kasar Equatorial Guinea ta daure dan Shugaban Kasar a kurkuku kan sayar da jirgin sama mallakin kasar ba bisa ka’ida ba, sannan ya zuba kudaden a aljihunsa.
Alkalin kotun dai a ranar Laraba ya yanke hukuncin cewa dan Shugaban Kasar Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, mai suna Ruslan Obiang Nsue, zai shafe shekaru shida a gidan yari.
Sai dai kotun ta ce idan zai biya kudin jirgin da ya bace ba za a daure shi ba, kamar yadda Daraktan yada labarai na Kotun Kolin Kasar, Hilario Mitogo ya shaida wa ’yan jarida.
Kotun dai ta yanke wa Ruslan mai shekaru 50 a duniya, wanda tsohon shugaban kamfanin jiragen samar kasar mai suna Ceiba Intercontinental hukuncin ne bisa laifin sayar da jirgin kasar mai suna ATR 72-500 ga wani kamfanin kasar Spain, sannan ya zuba kudin a aljihunsa.
A shekara ta 2023 an yi masa daurin talala bisa umarnin Mataimakin Shugaban Kasar, wanda shi ma dan uwansa ne na jini kuma dan shugaban kasar.
Kotun dai ta ce wanda aka yanke wa hukuncin zai iya kauce wa daurin idan ya biya tarar Dalar Amurka 255,000, kwatankwacin sama da Naira miliyan 382 ga kamfanin jiragen sannan ya biya tara ga gwamnati.
Sai dai kotun ta wanke shi daga wasu zarge-zargen na almundahana da halatta kudaden haram.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Shugaban Kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Sarakunan suna bada haɗin kai wajen tafiyar da harkokin gwamnatin ƙasarsu, suna kuma jin basu tare da wata matsala ba tare da matsayinsu. Yawancin Sarakuna da kuma wasu manyan msu Sarautar gargajiya bugu da ƙari suna cikin majlisar dattawa a lokacin.
Duk kuma wani lokaci da Sarakunan gargajiya suka fahimci suna fuskantar barazana dangane da tsaronsu, ta haka ne za su fara wasu tafiye- tafiye basu nan basu can, wanda idan ba sa’a aka yi ba, kusan ƙarshen ƙasar ke nan a matsayinta na tarayyar Nijeriya a lokacin. Duk wani ƙoƙarin da Abubbakar Tafawa Balewa ya yi na kasancewa ya zama kamar yadda Kwame Nkrumah na Ghana, wanda a zamaninsa kome ya ce daidai ne sai an bi ko amfani da shi, irin hakan ba zai iya haifar da ɗa mai ido ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp