Rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC a Gombe
Published: 24th, August 2025 GMT
Jam’iyyar ADC a Jihar Gombe, ta sanar da korar tsohon ɗan takarar gwamnanta na shekarar 2015, Nafiu Bala, bisa zargin yi mata zagon ƙasa.
Shugaban ADC na jihar, Auwal Abba Barde, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da ya gudana a Gombe.
An harbe masu garkuwa da mutane 3 a Kebbi Mutum 6 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a SakkwatoA cewarsa, kwamitin ladabtarwa na unguwar Nasarawo ya binciki Bala, inda ya same shi da laifukan cin amanar jam’iyyar wanda hakan ya saɓa wa dokokinta.
Ya ce an gayyaci Bala domin ya kare kansa a gaban kwamitin amma ya ƙi bayyana.
Barde ya ƙara da cewa kwamitin zartarwa na jihar, ya tabbatar da wannan hukunci, kuma sun aike wa shugabancin jam’iyyar na ƙasa domin ɗaukar matakin na gaba.
Haka kuma ya bayyana cewa wasu daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar a jihar an tsige su daga muƙamansu.
Duk da ɗaukar wannan mataki, Nafiu Bala, ya yi watsi da shi, ya bayyana cewa shi ne halastaccen shugaban riƙo na jam’iyyar na ƙasa.
Ya ce an zaɓe shi ne bisa tsarin jam’iyyar bayan taron gangamin da aka gudanar.
Bala, ya ƙara da cewa tun daga shekarar 2022 aka kori Auwal Abba Barde daga jam’iyyar, don haka ba shi da ikon ladabtar da shi ko ɗaukar wani mataki a kansa.
Ya yi nuni da cewa kundin tsarin mulkin ADC da dokokin Najeriya sun buƙaci duk wanda aka kora daga jam’iyya ya sake yin rajista daga matakin unguwa kafin ya dawo cikinta.
A cewarsa, hakan ya sa bai ɗauki hukuncin da aka ɗauka a kansa da muhimmanci.
Ya kuma bayyana cewa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta amince da shi a matsayin shugaban riƙo na jam’iyyar na ƙasa.
Bala, ya jaddada cewa zai ci gaba da jagoranci domin tabbatar da gaskiya da haɗin kai a jam’iyyar, sannan ya gargaɗi waɗanda ke ƙoƙarin tada zaune-tsaye a ADC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jam iyya a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.